Skip to main content

Posts

KALAMAN GWAMNA BELLO MUHAMMAD MATAWALLE NA JIHAR ZAMFARA A KAN TSOHON GWAMNA AA YARI

a falsafa irin ta siyasa wanda muke gani tana gudana a daidai wannan lokaci, bayyane take karara kalaman gwamnan jihar Zamfara (Rt,Hon Bello Muhammad Matawallen Maradun) jan kunne ne ga tsohon gwamnan jihar Zamfara (Dr, Hon Abdul-aziz Abubakar Yari shattiman Zamfara) kuma jan kunne ne ga dukkanin wani mai kokarin yin tugu ga zaman lafiyar da ake ganin jihar ta samu tun bayan kame madafun ikon da shi wannan gwamna Bello Matawalle yayi. Idan muka yi dubi a mahanga irin ta siyasa zamu ga cewa mutum zai iya yin duk wani abu domin cimma wata manufa ko da kuwa hakan zai iya bakanta ran dubban al'umma, faifan bidiyon da ya bayyana a ranar Alhamis 21 ga watan Satumbar 2019 ya ja hankulan dubban mutane a sassa daban-daban na kasar nan da wasu kasashen ketare, inda an ka gano gwamnan Bello Matawalle shi da kansa ya na bayyana irin ƙwaƙwaran matakin da zai dauka ga tsohon gwamnan AA Yari. Idan dai zamu iya tunawa gwamnan ya sha kiran taron 'ya'yan jam'iyyarsa ta APC a gid...

Gidauniyar Yazeed Danfulani ta dau nauyin karatun yara 20

* YAZEED DANFULANI TRUTS FUND * _wannan foundation mai suna a sama karkashin kulawar * (Alh. Yazeed Shehu Dan Fulani) * ya ziyarci fadar masarautar Mayana a gundumar Mayana a karamar hukumar mulkin Gusau a jihar Zamfara, domin neman tubarrakin masarautar, hadi da bayyana dukkanin kuduroran wannan kungiya wajen bada muhimmiyar gudunmuwa a bangaren ilimi. _A lokacin ziyarar an tattauna muhimman jawabai akan kudurin ganin yara masu tasowa sun samu nagartacciyar tarbiyya, da kuma tasowa da kyakkyawar mu'amala a cikin al'umma, kasancewar yaro na kowa ne!_ _Bayan nan an gabatar da yara Kanana Mata da Maza har su Ashirin 20 wadanda an ka dinkawa uniform hadi da basu kayan karatu kyauta da daukar nauyin karatunsu a matakin Primary a cikin gundumar ta mayana._ _Ilimi shine ƙashin bayan ci gaban kowace al'umma a duniya! A dalilin haka yasa wannan * Foundation * ya himmatu wajen ganin yara sun samu ilimi don tallafawa kansu da al'umma._ _Masar...

Najeriya Barka da samun 'yancin kai shekara59

Najeriya Kasa mai albarka, hakika muna godiya ga Allah ta'ala da ya nuna mana Najeriya ta cika shekara 59 da samun 'yancin kai daga turawan mulkin mallaka na Burtaniyya, duk wani dan kasa na gari ya zama wajibi yayi murna da wannan rana, domin abun alfahari ce ga 'yan Najeriya kwata. Ya zama wajibi muyi jinjina ga 'yan mazan jiya, wato  Sir Ahmadu Bello Sardaunan sakkwato. Da Sir Abubakar Tafawa ɓalewa, da sauran wadanda lokaci ba zai bani damar zaiyana su ba,  wadannan jajirtattun mutane sun taka muhimmiyyar raya wajen hada kan kasar nan domin kasancewa turba daya, kuma a matsayin tsintsiya madauri daya. Muna addu'ar Allah yayi masu sakayya da gidan al'janna. A bisa wannan ya kamata shuwagabannin wannan zamani suyi kwaikwayon kyakkwan halayen wadannan bayin Allah domin ganin kasar nan ta ci gaba da zama a matsayin turba daya, idan har ana son ganin kasar nan ta cigaba da zama a matsayin abu daya, to lallai ne shuwagabannin kasar su sanya kishin kasa gaba ...

Makomar Najeriya a kasashen duniya a taron koli na majalisar dinkin duniya

KO NAJERIYA TA TABA SAMUN WANI ALFANU A CIKIN TARON DA TAKE HALLARTA A ZAUREN MAJALISAR DINKIN DUNIYA?                Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya Kamar yadda ake ci gaba da gudanar da ire-iren wadannan tarurruka a shekara-shekara wanda wannan shine 74 a cikin jerin tattaunawar da ake a zauren majalisar dinkin duniya. Najariya Kasa ce Mai albarka kuma tana da kima da daraja a idon duniya Wanda hakan ya sa itama tana daya daga cikin manyan baki masu jawabi a cikin zauren na majalisar. Taron Wanda yake gudana, kuma manufar taron na bana shine kalubale na sauyin yanayi, Wanda ake kokarin ganin an tallafawa kasashen duniya masu fama da wannan matsalar, kuma a cikin taron har wasu gwamnatocin kasashen duniya sun Fara bayar da tallafinsu a cikin wannan shirin, shirin Wanda ya samu bakuntar kasashe 66 a bana.                 Shugaban majalisar dinkin duniya Antonio kutaresh Manyan kasashen da ...

Zuwa Ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

Assalamu alaikum, da fatan alheri ga dukkan wanda zai karanta wannan rubutu nawa, ina fatan wannan rubutu nawa zai kai ga hannun Shugaban ƙasar Najeriya Muhammadu Bahari, na dubi yiwuwar wannan rubutun ne domin kara yin tuni ga Muhammadu Bahari akan Arewa, wanda shi kansa ɗan yankin Arewa ne, kuma Arewar tana cikin wani hali, lallai ne ayi duk mai yiwuwa wajan dawo da martabarta. Duk da kasancewar sha'anin mulki abu ne mai matukar sarkakiya da wahalar gaske, duk da kasancewar munsan kana iya ƙoƙarinka wajan ganin kafitar da ƙasar nan ga tudunmun tsira, amma ya kamata a dubi arewa da idon Rahama, ya kamata a samarwa da arewa abubuwa masu matuƙar muhimmancin gaske wanda ko bayan baka a samun kujerar shugabancin ƙasar nan duk lokacin da aka tuna da abubuwan na alheri za'a rika maka addu'a da fatan alheri. Ganin wannan shine wa'adi na ƙarshe ga reka, kuma shine dama ta ƙashe wadda ya kamata kayi amfani da ita wajen maida akalar tunanenka a yankinka, lallai ne a gina...

Ra'ayin mai Apple, a kan masu kokarin tada zaune tsaye

Tsaro; wani babban tsani ne wanda shine ake bi wajan samuwar dukkan abubuwan rayuwa, kuma sai da shine sannan komai na rayuwa yake tafiya daidai, tsaro wani babban ginshiƙi ne a rayuwar al'umma. Babu wata ƙasa a duniya da zata samu ci gaba, ko ta samu ci gaba, ko take cikin samun ci gaba ba tare samuwar zaman lafiya ba. Wannan ne yasa mun ka himmatu wajan gwaggwarmayar ganin jihar Zamfara ta samu sauyi ta fuskar gwamnati a bisa la'akari da yadda waccen gwamatin da ta shuɗe ta gaza matuƙa ainun wajan kare rayukan al'umma haɗi da dukiyoyinsu, mun ka tsaya kai-da-fata wajan ganin an samu kyakkyawan sauyi domin al'ummar jihar Zamfara su riƙa kwana da idanu biyu-biyu ba tare da wani ɗar a zuciya ba. Kuma cikin ikon Allah, sai da muka ga haƙarmu ta cimma ruwa a wannan fannin. Wannan ne yasa mun ka koma gyefe daya munka zura idanu muna kallon kamun ludayin wannan gwamatin kasancewar mun ga da gaske take wajan samar da tsaro a cikin kwaryar jihar Zamfara haɗi da wasu ma...

Babban taron kungiyar Remarkable Karo na Hudu ya kayatar

              'ya'yan kungiyar remarkable bayan kammala taro. _Wannan kungiya mai suna a sama tayi taronta kamar yadda ta saba, kuma an kammala cikin nasara da kwanciyar hankali, an tattauna akan muhimman abubuwa masu matukar amfani ga Al'umma Musamman marasa gata._ _Daga cikin ayyukan da kungiyar za ta maida hankali a Kai shine tallafawa al'majirai masu karatun allo, don ba da gudumuwa ga abinda ya shafi addini. Bayan kammala hakan daidai iyawarmu da kuma karfinmu,  Abu na gaba shine kungiya zata zagaya domin gaisuwar ban girma hadi da neman shawarwari ga dattawan kungiyar don a gudu tare a tsira tare._                  Shugaban kungiyar tare malamin jami'a na birnin kebbi         _Idan ba son juna hadin Kai da wuya kaga ya dore, ko shakka babu yana da kyau mu kasance masu hadin Kai da nuna kishi wa junanmu, hakan zai bamu damar cin kowace irin nasara, dole ne mu nis...