Skip to main content

Gidauniyar Yazeed Danfulani ta dau nauyin karatun yara 20


*YAZEED DANFULANI TRUTS FUND*


_wannan foundation mai suna a sama karkashin kulawar *(Alh. Yazeed Shehu Dan Fulani)* ya ziyarci fadar masarautar Mayana a gundumar Mayana a karamar hukumar mulkin Gusau a jihar Zamfara, domin neman tubarrakin masarautar, hadi da bayyana dukkanin kuduroran wannan kungiya wajen bada muhimmiyar gudunmuwa a bangaren ilimi.


_A lokacin ziyarar an tattauna muhimman jawabai akan kudurin ganin yara masu tasowa sun samu nagartacciyar tarbiyya, da kuma tasowa da kyakkyawar mu'amala a cikin al'umma, kasancewar yaro na kowa ne!_


_Bayan nan an gabatar da yara Kanana Mata da Maza har su Ashirin 20 wadanda an ka dinkawa uniform hadi da basu kayan karatu kyauta da daukar nauyin karatunsu a matakin Primary a cikin gundumar ta mayana._


_Ilimi shine ƙashin bayan ci gaban kowace al'umma a duniya! A dalilin haka yasa wannan *Foundation* ya himmatu wajen ganin yara sun samu ilimi don tallafawa kansu da al'umma._

_Masarautar tayi jinjina ga wannan kungiya hadi da addu'ar Allah ya sakawa wannan bawan Allah da mafificin alheri, haka masarautar tayi kira ga sauran ɗaiɗaikun jama'a da ma kungiyoyi da suyi koyi da wannan kungiyar wajen tallafawa gajiyayyu da marayu da marasa gata a cikin al'umma._


_Bayan kungiyar ta kammala baje kolin  abun alherin a gaban masarautar, ta zarce *makarantar Birnin Ruwa Primary School* domin tasa keyar yaran da sun ka amfana da wannan tallafi a gaba don hannintasu ga shugaban makarantar ta birnin ruwa. *Yazeed Trust Fund* tayi kicibus da shugaban makarantar in da shima ya bayyana farin cikinsa a kan wannan kokari, inda yace tun lokacin da ya fara koyarwa a makaranta a shekara 1999 har zuwa wannan lokaci bai taba ganin wata kungiyar da tayi irin wannan nazarin ba, shugaban kungiyar Yazeed Trust Fund Comrade Rufa'i Bala U&B yace wannan kungiya a shirye take ka'in-da-na'in wajan bada tallafi iya karfinsu domin ganin al'umma sun cigaba. Rufa'i Bala U&B yana tare da rakiyar wasu daga cikin shuwagabannin kungiyar da sauran Exco da membobin kungiyar a wajan yin wannan muhimmin aikin alheri._
_Idan dai za a iya tunawa ko ba a manta ba wannan Foundation ya lashi takobin shiga lunguna da suƙunan wannan karamar hukuma domin bada taimako daidai gwargwadon hali. Ko yaushe taken tafiyar dai shine tallafawa yara masu darajja, da wannan muke rokon Allah ta'ala ya sanya albarka da alheri ga wadannan yara yayi wa rayuwarsu albarka._


*Fatan Alheri ga Yazeed Trust Fund*


_*Daga Nura Mai Apple Reporter Media News*_



Copyright@nuramaiapple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...