Skip to main content

Ra'ayin mai Apple, a kan masu kokarin tada zaune tsaye



Tsaro; wani babban tsani ne wanda shine ake bi wajan samuwar dukkan abubuwan rayuwa, kuma sai da shine sannan komai na rayuwa yake tafiya daidai, tsaro wani babban ginshiƙi ne a rayuwar al'umma. Babu wata ƙasa a duniya da zata samu ci gaba, ko ta samu ci gaba, ko take cikin samun ci gaba ba tare samuwar zaman lafiya ba.

Wannan ne yasa mun ka himmatu wajan gwaggwarmayar ganin jihar Zamfara ta samu sauyi ta fuskar gwamnati a bisa la'akari da yadda waccen gwamatin da ta shuɗe ta gaza matuƙa ainun wajan kare rayukan al'umma haɗi da dukiyoyinsu, mun ka tsaya kai-da-fata wajan ganin an samu kyakkyawan sauyi domin al'ummar jihar Zamfara su riƙa kwana da idanu biyu-biyu ba tare da wani ɗar a zuciya ba.

Kuma cikin ikon Allah, sai da muka ga haƙarmu ta cimma ruwa a wannan fannin. Wannan ne yasa mun ka koma gyefe daya munka zura idanu muna kallon kamun ludayin wannan gwamatin kasancewar mun ga da gaske take wajan samar da tsaro a cikin kwaryar jihar Zamfara haɗi da wasu makwaftan jihar, ƙokarin gwamna (Rt. Hon Bello Muhammad Mon Matawallen Maradun) na jihar Zamfara wajan samar da tsaro a jihar Zamfara abun yabawa ne, kuma dole a jinjina masa a wannan fannin.


Duk wani Bazamfare yaji matuƙar daɗi lokacin da yaga zaman lafiya yana gudana, wannan ne yaja hankulan talakawa a sassa daban-daban na jihar ta Zamfara da wasu jihohi damin yiwa gwamna addu'o'i na musamman, don samun ɗorewar zaman lafiya a jihar ta Zamfara da Arewa da Najeriya baki daya.

To sai dai kokarin wasu ɓata gari masu son maida hannun agogo baya, na son tada zaune tsaye, a sha'anin tsaron wani babban abun takaici ne, haɗi da tir da Allah waddai, kuma ya kama su san cewa Allah ya la'anci duk mai tada rigima da hargitsi a cikin al'umma, yana da kyau da muhimmanci muji tsoron Allah a cikin kowane irin al'amari na rayuwa, ya zama wajibi mu haɗa kai domin zaman wanzuwar zaman lafiya a  cikinmu, hakan zai yi tasiri wajan bunkasuwar jiharmu ta Zamfara har mu ciyar da wasu jihohi da dama na ƙasar nan.


Ƙalubalenku jami'an tsaro, lallai ne kuyi iya ƙokarinku wajan kara tashi tsaye da tanke ɗamarar binciken kwakwaf da amfani da kwarewarku, da hikimarku, wajan zaƙulo bayanan sirri, na masu ƙoƙarin ganin sun banzarantar da tsaro a cikin jahar nan domin su fuskanci fushin hukuma a yanke musu hukunci daidai da abinda sun ka aikata, ko suke ƙokarin aikatawa.

Muna fatan samun dauwamammen Zaman lafiya a jihar Zamfara da Najariya baki daya. Fatan alheri da gwamnati jihar Zamfara.


Daga; Nura Mai Apple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

Ta kashe Mijin ta na aure

Ta kashe Mijin ta na aure Jami'an 'Yan Sanda sun damke wata mata mai shekara 42 ta kashe Mijin ta na aure a wata Unguwa a Garin Legas. Ana zargin Folashade Idoko da kashe Mijin ta a cikin gidan su. Jaridar Daily Post tace wannan mummunan abu ya faru ne a cikin Oto-Awori na Garin Legas. Marigayin dai Injiniya ne kuma tuni dai Jamia'an 'Yan Sanda su kayi ram da wannan mata. Mai gidan hayan da Iyalin su ke yace matar wanda malamar asibiti ce ta dade su na samun matsala da Mijin na ta amma yana hakuri. Kuma dai akwai kishin-kishin din cewa kishin jaraba ne ya sa ta kashe Mijin na ta. Matar dai tace tsautsayi aka samu wuka ta fadi a jikin sa ya mutu. Jami’an tsaro sun damke wani saurayi Ifeanyi Chukwu Maxwell Dike dauke da jikin wata yarinya da aka sace a makon jiya.