Skip to main content

Ra'ayin mai Apple, a kan masu kokarin tada zaune tsaye



Tsaro; wani babban tsani ne wanda shine ake bi wajan samuwar dukkan abubuwan rayuwa, kuma sai da shine sannan komai na rayuwa yake tafiya daidai, tsaro wani babban ginshiƙi ne a rayuwar al'umma. Babu wata ƙasa a duniya da zata samu ci gaba, ko ta samu ci gaba, ko take cikin samun ci gaba ba tare samuwar zaman lafiya ba.

Wannan ne yasa mun ka himmatu wajan gwaggwarmayar ganin jihar Zamfara ta samu sauyi ta fuskar gwamnati a bisa la'akari da yadda waccen gwamatin da ta shuɗe ta gaza matuƙa ainun wajan kare rayukan al'umma haɗi da dukiyoyinsu, mun ka tsaya kai-da-fata wajan ganin an samu kyakkyawan sauyi domin al'ummar jihar Zamfara su riƙa kwana da idanu biyu-biyu ba tare da wani ɗar a zuciya ba.

Kuma cikin ikon Allah, sai da muka ga haƙarmu ta cimma ruwa a wannan fannin. Wannan ne yasa mun ka koma gyefe daya munka zura idanu muna kallon kamun ludayin wannan gwamatin kasancewar mun ga da gaske take wajan samar da tsaro a cikin kwaryar jihar Zamfara haɗi da wasu makwaftan jihar, ƙokarin gwamna (Rt. Hon Bello Muhammad Mon Matawallen Maradun) na jihar Zamfara wajan samar da tsaro a jihar Zamfara abun yabawa ne, kuma dole a jinjina masa a wannan fannin.


Duk wani Bazamfare yaji matuƙar daɗi lokacin da yaga zaman lafiya yana gudana, wannan ne yaja hankulan talakawa a sassa daban-daban na jihar ta Zamfara da wasu jihohi damin yiwa gwamna addu'o'i na musamman, don samun ɗorewar zaman lafiya a jihar ta Zamfara da Arewa da Najeriya baki daya.

To sai dai kokarin wasu ɓata gari masu son maida hannun agogo baya, na son tada zaune tsaye, a sha'anin tsaron wani babban abun takaici ne, haɗi da tir da Allah waddai, kuma ya kama su san cewa Allah ya la'anci duk mai tada rigima da hargitsi a cikin al'umma, yana da kyau da muhimmanci muji tsoron Allah a cikin kowane irin al'amari na rayuwa, ya zama wajibi mu haɗa kai domin zaman wanzuwar zaman lafiya a  cikinmu, hakan zai yi tasiri wajan bunkasuwar jiharmu ta Zamfara har mu ciyar da wasu jihohi da dama na ƙasar nan.


Ƙalubalenku jami'an tsaro, lallai ne kuyi iya ƙokarinku wajan kara tashi tsaye da tanke ɗamarar binciken kwakwaf da amfani da kwarewarku, da hikimarku, wajan zaƙulo bayanan sirri, na masu ƙoƙarin ganin sun banzarantar da tsaro a cikin jahar nan domin su fuskanci fushin hukuma a yanke musu hukunci daidai da abinda sun ka aikata, ko suke ƙokarin aikatawa.

Muna fatan samun dauwamammen Zaman lafiya a jihar Zamfara da Najariya baki daya. Fatan alheri da gwamnati jihar Zamfara.


Daga; Nura Mai Apple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...