Skip to main content

Najeriya Barka da samun 'yancin kai shekara59



Najeriya Kasa mai albarka, hakika muna godiya ga Allah ta'ala da ya nuna mana Najeriya ta cika shekara 59 da samun 'yancin kai daga turawan mulkin mallaka na Burtaniyya, duk wani dan kasa na gari ya zama wajibi yayi murna da wannan rana, domin abun alfahari ce ga 'yan Najeriya kwata.

Ya zama wajibi muyi jinjina ga 'yan mazan jiya, wato  Sir Ahmadu Bello Sardaunan sakkwato. Da Sir Abubakar Tafawa ɓalewa, da sauran wadanda lokaci ba zai bani damar zaiyana su ba,  wadannan jajirtattun mutane sun taka muhimmiyyar raya wajen hada kan kasar nan domin kasancewa turba daya, kuma a matsayin tsintsiya madauri daya. Muna addu'ar Allah yayi masu sakayya da gidan al'janna.

A bisa wannan ya kamata shuwagabannin wannan zamani suyi kwaikwayon kyakkwan halayen wadannan bayin Allah domin ganin kasar nan ta ci gaba da zama a matsayin turba daya, idan har ana son ganin kasar nan ta cigaba da zama a matsayin abu daya, to lallai ne shuwagabannin kasar su sanya kishin kasa gaba koma bayan bukatun kansu dana 'yan uwansu.

Kowane dan Ƙasa yana da irin rawar zai iya takawa wajan ciyar da kasar a gaba, ta hanyar bayar da hadin kai, ta fuskar zaman lafiya da hadin kan juna, da nuna da'a da halin dattako a duk inda ya tsintsi kansa.

Najeriya kasa ce mai matukar ƙima da kwarjini a idanun duniya, to idan muna son kasar nan ta cigaba da kasancewa a haka, to sai mun tsayu haikan gaskiya da gaskiya, mun yi aiki tare hadi da son juna, don kasar ta cigaba da rike kambunta.

Sai malamai na addinai daban-daban da muke da su a cikin kasar nan sun himmatu wajen kiraye-kiraye ga mabiyansu, su nuna musu hanyar gaskiya hadi da sanar da su tsantsar gaskiya, domin samun hadin kan kasa ta hakan ne arzikin kasar nan zai samu bunkasa, kasancewar Allah yayi wa 'yan Najeriya hikima da fasaha da sanin dabaru daban-daban, muna fatan Allah ya cigaba da saukar da albarka a cikin Najeriya.

Mutanen da Allah ya dorawa alhakin kula da talakawa wato shugabanninmu ya kamata su kara tanke damarar tallafa wa 'yan ƙasa don inganta rayuwarsu domin ganin an tafi da kowa bai daya.


Ina amfani da wannan damar domin fatan alheri ga Shugaban Kasar Najeriya Muhammdu Buhari da Mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo, da dukkanin gwamnonin Najeriya baki daya.

Allah ya karo albarka ga kasa ta Najeriya da arziki mayilwaci.

Muna murna da samun yancin Kai daga turawan mulkin mallaka na Burtaniyya !

Daga Nura Muhammad Mai Apple, Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...