Skip to main content

Najeriya Barka da samun 'yancin kai shekara59



Najeriya Kasa mai albarka, hakika muna godiya ga Allah ta'ala da ya nuna mana Najeriya ta cika shekara 59 da samun 'yancin kai daga turawan mulkin mallaka na Burtaniyya, duk wani dan kasa na gari ya zama wajibi yayi murna da wannan rana, domin abun alfahari ce ga 'yan Najeriya kwata.

Ya zama wajibi muyi jinjina ga 'yan mazan jiya, wato  Sir Ahmadu Bello Sardaunan sakkwato. Da Sir Abubakar Tafawa ɓalewa, da sauran wadanda lokaci ba zai bani damar zaiyana su ba,  wadannan jajirtattun mutane sun taka muhimmiyyar raya wajen hada kan kasar nan domin kasancewa turba daya, kuma a matsayin tsintsiya madauri daya. Muna addu'ar Allah yayi masu sakayya da gidan al'janna.

A bisa wannan ya kamata shuwagabannin wannan zamani suyi kwaikwayon kyakkwan halayen wadannan bayin Allah domin ganin kasar nan ta ci gaba da zama a matsayin turba daya, idan har ana son ganin kasar nan ta cigaba da zama a matsayin abu daya, to lallai ne shuwagabannin kasar su sanya kishin kasa gaba koma bayan bukatun kansu dana 'yan uwansu.

Kowane dan Ƙasa yana da irin rawar zai iya takawa wajan ciyar da kasar a gaba, ta hanyar bayar da hadin kai, ta fuskar zaman lafiya da hadin kan juna, da nuna da'a da halin dattako a duk inda ya tsintsi kansa.

Najeriya kasa ce mai matukar ƙima da kwarjini a idanun duniya, to idan muna son kasar nan ta cigaba da kasancewa a haka, to sai mun tsayu haikan gaskiya da gaskiya, mun yi aiki tare hadi da son juna, don kasar ta cigaba da rike kambunta.

Sai malamai na addinai daban-daban da muke da su a cikin kasar nan sun himmatu wajen kiraye-kiraye ga mabiyansu, su nuna musu hanyar gaskiya hadi da sanar da su tsantsar gaskiya, domin samun hadin kan kasa ta hakan ne arzikin kasar nan zai samu bunkasa, kasancewar Allah yayi wa 'yan Najeriya hikima da fasaha da sanin dabaru daban-daban, muna fatan Allah ya cigaba da saukar da albarka a cikin Najeriya.

Mutanen da Allah ya dorawa alhakin kula da talakawa wato shugabanninmu ya kamata su kara tanke damarar tallafa wa 'yan ƙasa don inganta rayuwarsu domin ganin an tafi da kowa bai daya.


Ina amfani da wannan damar domin fatan alheri ga Shugaban Kasar Najeriya Muhammdu Buhari da Mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo, da dukkanin gwamnonin Najeriya baki daya.

Allah ya karo albarka ga kasa ta Najeriya da arziki mayilwaci.

Muna murna da samun yancin Kai daga turawan mulkin mallaka na Burtaniyya !

Daga Nura Muhammad Mai Apple, Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...