Skip to main content

KALAMAN GWAMNA BELLO MUHAMMAD MATAWALLE NA JIHAR ZAMFARA A KAN TSOHON GWAMNA AA YARI




a falsafa irin ta siyasa wanda muke gani tana gudana a daidai wannan lokaci, bayyane take karara kalaman gwamnan jihar Zamfara (Rt,Hon Bello Muhammad Matawallen Maradun) jan kunne ne ga tsohon gwamnan jihar Zamfara (Dr, Hon Abdul-aziz Abubakar Yari shattiman Zamfara) kuma jan kunne ne ga dukkanin wani mai kokarin yin tugu ga zaman lafiyar da ake ganin jihar ta samu tun bayan kame madafun ikon da shi wannan gwamna Bello Matawalle yayi.

Idan muka yi dubi a mahanga irin ta siyasa zamu ga cewa mutum zai iya yin duk wani abu domin cimma wata manufa ko da kuwa hakan zai iya bakanta ran dubban al'umma, faifan bidiyon da ya bayyana a ranar Alhamis 21 ga watan Satumbar 2019 ya ja hankulan dubban mutane a sassa daban-daban na kasar nan da wasu kasashen ketare, inda an ka gano gwamnan Bello Matawalle shi da kansa ya na bayyana irin ƙwaƙwaran matakin da zai dauka ga tsohon gwamnan AA Yari.

Idan dai zamu iya tunawa gwamnan ya sha kiran taron 'ya'yan jam'iyyarsa ta APC a gidansa dake Talatar Mafara domin tattaunawa akan abubuwa mabambanta, wanda hakan yakan kara tunzura magoya bayansa da yin wasu batutuwa na daban. Babu ko shakka sha'ani irin na tsaro bai kamata a siyasantar da shi ba, domin idan har abinda gwamnan jihar Zamfara yake hasashe ya tabbata gaskiya, babu shakka wannn ya kasance kamar cin amanar kasa ne.


Tsarin zaman lafiya abu ne wanda duk a duniya babu wata kasa da ba ta yin na'am da shi, kuma babu wata kasa a duniya da  zata lamunci safgar ta'addanci domin babban laifi ne, kuma cin amanar kasa ne, to uwa-uba a Najeriya wanda zaman lafiyar ta yake tangal-tangal, musamman a Arewa wanda tafi fuskantar kalubale a sha'anin tsaro da sauran abubuwa na daban. Duk dan Jihar Zamfara wanda Da ya san inda aka fito, baya marhabun da duk wani tsari wanda zai shafi tada zaune tsaye.

Neman Zaman lafiya........

 muna kira da babbar murya ga gwamnatin jihar Zamfara da duk wani mai alhakin samar da tsaro a jihar Zamfara da cewa lallai ne ayi duk mai yiwuwa domin kara zage damtse wajan ganin zaman lafiya ya samu gindin zama a jihar nan. A na siyasantar da komai amma ban da sha'anin tsaro, domin rayukan al'umma ba wasa bane, kuma sai da al`ummar ne  sannan kowane irin shugaba zai iya gudanar da mulkinsa.

Lallai kowane shugaba ya sanya tsoron Allah a cikin al'amurransa domin ganin jihar nan ta kai ga tudunmun tsira. Sa ido kan sha'anin mulki nauyi ne wanda ya rataya a wuyan masu shugabantar al'umma a matakai daban-daban, kuma inkiya, ko hannunka mai sanda yana da muhimmancin gaske a sha'anin a shugabanci.

Muna bada shawara ga al'ummar jihar Zamfara a kan muhimmancin zaman lafiya a cikin al'umma. Duk wata ƙasa da ta samu haɓaka da ci gaba a duniya, ci gaban bai samu ba sai da zaman lafiya. Su kansu waɗanda ake amfani da su wajan tayar da ƙayar baya, ana amfani da su ne kawai domin cimma wata manufa wanda kuma hakan babban kuskure ne kuma cin amanar ƙasa ne.


Babu ko shakka kalaman gwamnan a daidai wannan gaɓar yayi a lokacin da ya dace, domin shi icce tun yana danye ake lankwasashi.


Mafita ......

Riga kafin wannan babban kalubale shi ne; lallai ne gwamnati tayi humɓasa wajan tashi tsaye tayi tsayuwar tsayin daka wajan bayar da ilimi a cikin al'umma domin jahilci na taka gagarumar gudunmuwa a fannin ta'addanci, haɗi da wayar da kan al'umma akan alfanun zaman lafiya da kuma irin muhimman abubuwan da zaman lafiya ke kawowa a sanadiyar zaman lafiya, hakan zai taimaka matuƙa ainun wajan samun haɗin kan al'umma domin a zauna lafiya.

A ƙarshe ina addu'ar samun dauwamammen zaman lafiya a cikin jihar Zamfara da Najeriya baki daya.


Daga Nura Muhammad Mai Apple


Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...