Skip to main content

Zuwa Ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.



Assalamu alaikum, da fatan alheri ga dukkan wanda zai karanta wannan rubutu nawa, ina fatan wannan rubutu nawa zai kai ga hannun Shugaban ƙasar Najeriya Muhammadu Bahari, na dubi yiwuwar wannan rubutun ne domin kara yin tuni ga Muhammadu Bahari akan Arewa, wanda shi kansa ɗan yankin Arewa ne, kuma Arewar tana cikin wani hali, lallai ne ayi duk mai yiwuwa wajan dawo da martabarta.

Duk da kasancewar sha'anin mulki abu ne mai matukar sarkakiya da wahalar gaske, duk da kasancewar munsan kana iya ƙoƙarinka wajan ganin kafitar da ƙasar nan ga tudunmun tsira, amma ya kamata a dubi arewa da idon Rahama, ya kamata a samarwa da arewa abubuwa masu matuƙar muhimmancin gaske wanda ko bayan baka a samun kujerar shugabancin ƙasar nan duk lokacin da aka tuna da abubuwan na alheri za'a rika maka addu'a da fatan alheri.

Ganin wannan shine wa'adi na ƙarshe ga reka, kuma shine dama ta ƙashe wadda ya kamata kayi amfani da ita wajen maida akalar tunanenka a yankinka, lallai ne a gina arewa da abubuwan more rayuwa, da haɓɓaka hulɗar kasuwanci da farfaɗo da manyan kwamfanonin arewa, wanda hakan zaisa dubban matasa su samu ayyukan yi, babu shakka mun san kayi ƙoƙari wajan samar da ayyukanyi ga matasa musamman samar da shirin nan na N-Pawer da sauransu, amma gaskiya hakan ba zai wadatar ba.

Shugaba Bahari ka sani babu wani wanda ya nuna maka soyayya ta gaskiya ta zahiri kamar mutanen Arewa, babu shakka yana da kyau ka mayar musu da biki, har yanzu akwai dubban matasa a arewa waɗanda basu da sana'ar yi, kawai suna zaman kashe wando, wanda hakan babban koma baya ne, shugaban Buhari arewa tana cikin matuƙar buƙatar neman taimakonka.

Shugaba Bahari yana da kyau ka yaye duk wani hijabi dake tsakaninka da talakawanka, domin kaima ka hangosu kamar yadda suma sun kayimaka kara, muna fatan zaka dubi makomar arewa da 'yan arewa, kuma ka gina arewa kafin karshe wa'adin mulkinka, muna fatan Allah yasa ka fahimci irin soyayyar da 'yan arewa sun ka nuna maka, domin share musu hawayensu.


Fatan alheri ga reka da kuma masu son arewa, da kishin mutanen arewa.


Daga Nura Muhammad mai Apple. Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.