Skip to main content

Makomar Najeriya a kasashen duniya a taron koli na majalisar dinkin duniya

KO NAJERIYA TA TABA SAMUN WANI ALFANU A CIKIN TARON DA TAKE HALLARTA A ZAUREN MAJALISAR DINKIN DUNIYA?
               Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya


Kamar yadda ake ci gaba da gudanar da ire-iren wadannan tarurruka a shekara-shekara wanda wannan shine 74 a cikin jerin tattaunawar da ake a zauren majalisar dinkin duniya. Najariya Kasa ce Mai albarka kuma tana da kima da daraja a idon duniya Wanda hakan ya sa itama tana daya daga cikin manyan baki masu jawabi a cikin zauren na majalisar.

Taron Wanda yake gudana, kuma manufar taron na bana shine kalubale na sauyin yanayi, Wanda ake kokarin ganin an tallafawa kasashen duniya masu fama da wannan matsalar, kuma a cikin taron har wasu gwamnatocin kasashen duniya sun Fara bayar da tallafinsu a cikin wannan shirin, shirin Wanda ya samu bakuntar kasashe 66 a bana.
                Shugaban majalisar dinkin duniya Antonio kutaresh


Manyan kasashen da sun kafi kowa morewa tarurrukan Wanda majalisar dinkin duniya take shiryawa 'yan tsiraru ne, daga ciki akwai; Amurka da Rasha, da Japan, da China, da kuma Prance,  amma har yanzu Najariya babu wani alfanu da samu ko take samu a cikin tarurrukan.

A jiya ne Shugaban kasar Najariya Muhammadu Buhari yayi cikakken jawabi a wajan taron har na tsawon Mintuna 15:40, duk da kasancewar ya tabo muhimman abubuwa daban-daban, daga ciki harda na neman taimakon kasashen duniya wajan ceto tafkin Chadi Wanda yake cikin barazana,  to mu a mahangarmu ta masu nazarin abubuwan yau da kullum, muna ganin ko a wannan Karon haka za'a watse taron ba tare da mun amfana da komai ba, duk da mataimakiyyar Shugaban majalisar Hajiya Amina Muhammad 'yar Najeriya ce, to amma hakan baya saka mata Kishin kasar da kuma tunanen taimaka mata.

      Lokacin da shugaba Buhari na Najeriya yake jawabi


A karshe muna fatan taron na wannan Karon zai amfanar da Najeriya, kuma ya sa Tana cikin kasashen da zasu ci moriyar wannan shirin.

Duk wani shiri ba zai yi tasiri ba har sai mu 'yan Najeriya mun hada kanmu a matsayin tsintsiya madauri daya, mun yaki wariyar kabilanci, da rashin son junanmu, mun dawo mun hada Kai mun Samar da zaman lafiya a tsakaninmu, Sannan mu Kai ga kowane irin ci gaba.


Allah ya taimaki Najeriya da masu son ganin ta ci gaba.

Daga Nura Mai Apple, Gusau



Copyright@nuramaiapple2019

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...