Skip to main content

Posts

RA'AYIN MAI APPLE AKAN SIYASAR KANO

Assalamu alaikum, barkarmu da yau barka da wannan lokaci tare da fatan dukan masu bibiya ta a kafofin sadarwa daban-daban suna cikin koshin lafiya, ya a kaji da fama? Yau ra'ayin nawa zai maida hankali ne kachokan akan siyasar wata jiha daga cikin manyan jihohin Najeriya kuma jiha mafi yawan al'umma a Najeriya, wato jihar Margayi malam Aminu Wato Kano kenan. Tabbas jihar kano jiha ce wanda Allah madaukakin sarki ya arzuta ta da mutane masu hazaka da basira da kwazo da sanin ya kamata, sannan kanawa mutane ne, masu kawaici da nuna da'a da dattako. Tun farkon samuwar wannan kasar tamu, wato Najeriya, tun lokacin zamunna daban-daban da suka shude, Jihar kano sananniya ce wajen kokarinta na kawo dukan cigaban da za'ayi alfahari da ita, wanda a cikin jajircewar ta ne yasa Arewa tayi fice kuma ta samu daukaka ƙima da daraja a idon Duniya. Kamar dai yadda masu salon iya zance suke fada da cewa ''Kano Ta Dabo Tunbin Giwa yaro Ko Dame kazo Anfika'' ko shakk...

LABARIN SIRRI...... 'YAN SIYASAR AREWA

Daga; Nura Mai Apple Wasu daga cikin gwamnatocin Arewa Sun ware makuddan kudade domin sayen masu kada kuri'a, domin zarcewa a wa'adi na gaba, ko zarcewar magadan da zasu gadar kujerunsu a matakin gwamna ko 'yan majalisu. Bayanin sirrin ya fara bayyana ne daga wata majiya Mai kyau. Inda gwamnatocin suke amfani da kudaden baitin-malin gwamnati domin kaiwa ga nasarar 'yan takararsu. Ko shakka babu, Amfani da kudi wajen sauya bukatun masu kada kuri'a, wajen amfani da kuncin rayuwa da talaucin da ya addabi 'yan Arewa, wani babban abun koma baya ne ta fuskar demokaradiyyar kasar nan. Ya kamata hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa wato EFCC DA ICPC suyi iya kokarinsu wajen saka ido sosai ga gwamnatocin Arewa, domin dakile wannan gagarumar matsala. Yana daya daga cikin abinda yasa Masu hannu da shuni da 'yan siyasar kasar nan suke kiyayye da magance matsalar talauci a Najeriya. Allah Muna Addu'a da sunaye...

YA KAMATA JAM'IYYUN ADAWA A JIHAR ZAMFARA SU ƘAURACEWA BABBAN ZAƁEN GWAMNONI DA NA 'YAN MAJALISUN JIHA DAKE TAFE

Ko shakka babu; kamar yadda ta bayyana ƙarara a zaɓen da ya gudana na shugaban Ƙasa da na 'yan Majalisun tarayya a ranar 23 ga fabrairun makon da ya gabata, irin yadda anka samu tarin matsaloli wajen yin zaɓen, Jam'iyyar APC mai ƙarfin fada a ji a cikin jihar ta Zamfara ita tayi uwa, tayi makarɓiya a cikin zaɓen, ma'ana dai ina nufin jam'iyyar tayi amfani da karfin ikon da take da shi, wajen cin karanta ba babbaka a dukkanin inda aka gabatar da zaɓen duk da kasancewar ita shugabar zaɓe ta jihar Zamfara ta tabbatar da za'ayi zaɓe mai cike da sahihanci da tsafta wanda kowa zaiyi na'am da shi. A daidai lokacin da aka wayi garin safiyar zuwa runfunan zaɓe wato ranar Asabar, an samu wasu matsaloli, ta fuskar jinkirin kai kayan zaɓe da wuri, inda wasu rahotannin da muka samu daga wasu jihohin ƙasar nan daban-daban sun dade da fara jefa kuri'unsu, alhali kuma a nan jihar Zamfara ba'a kai kayan zabe ba, duk da tabbacin da hukumar shirya zabe ta ƙasa ta b...

JUYIN JUYA HALIN SIYASAR NAJERIYA YASA SUNAN ZAMFARA YA DUSASHE!

Daga; Nura Muhammad mai Apple, Gusau. Gagarumar ɓaraka, da muhawara mai zafin gaske, da musayar kalamai da suka kaure tsakanin Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya mai fafutikar ganin ya koma karagar mulkin Najeriya wa'adi na biyu. Da Madugun 'yan Adawar jam'iyyar PDP Wato Alh. Atiku Abubakar. yasa sunan Zamfara ya 'bace Bat, na inda anka kwana wajen Gwama sunayen 'yan takarar Jam'iyyar Apc Mai Mulki a Jihar Zamfara cikin jerin Jadawalin zaben da zai gudana, 'yan Kwanaki kadan masu zuwa! In ana babbakar Giwa ba'ajin ƙaurin bera. Irin yadda siyasar Kasar ta Ɗauki wani sabon salo, yasa kwata-kwata an daina labarin jihar ta Zamfara, balle musan ina ina aka kwana ta wannan ɓangaren. A gyefe duga kuwa, kamar saka sunayen 'yan takara daga jihar Zamfara zai kara sa dangantakar kara tsami matuƙa ainun, a ɓangarorin jam'iyyun guda biyu. Muna fatan za'ayi siyasa a Najeriya mai tsafta, bada gaba ba.  Muna fata kafin nan da wani ɗan lokaci ...

ZUWA GA MABARATAN ZAMANI A SOCIAL MEDIA WAƊANDA SUKA KOMA KARNUKAN 'YAN SIYASA!

Daga Nura Muhammad Mai Apple, Gusau. Yaɗa ƙarya don samun abin sakawa a baki, babban haɗari ne ga masu aikata hakan da manufar samun na cefane! Labarun bugu wanda ake kira da sunan labarun ƙanzon kurege suna matuƙar cin kare su babu babbaka a cikin wannan zamani da muke ciki. Duk abinda zakayi sai kayi abisa manufa guda biyu ! 1 farko shine; shin abinda kake ƙokarin aikatawa bai ci karo da addininka ba? shin idon har ka aikatashi ba zai jawo maka hushin Ubangiji ba? Idon har ka aikata abin zai amfani wani abu daga cikin addininka ko dai yaya? 2 menene dokokin ƙasa sunka yarje maka ka aikata wanda kuma dokokin sunka baka dukkanin kowace irin cikakkiyar dama. Idon aka samu waɗannan guda biyu a lokaci daya, to zai kyautu ka tsaya waje daya kayi dogon nazari da tunane domin dora kowane daya daga cikinsu abisa ma'aunin hankali sai ka banbance tsakanin aya da tsakuwa. Sanin kowane musulmi ne da cewa karya tana daya daga cikin abinda Allah Ta'ala yayi hani da ita kuma ha...

RASHIN GUDANAR DA ZAƁE MAFI YAWA DAGA CIKIN MUTANE SUN TAFKA BABBAR ASARA!

Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau Hukuncin da hukumar Zaɓe ta ƙasa mai cin gashin kanta da ɗauka na ɗage babban zaɓen da ake sa ran gudanarsa a yau wani babban ƙalubale ne, sannan babu wani gamsashen madogara ko hujja wanda hukumar zatayi godogo da ita, wanda zaisa har mafi yawa daga cikin mutanen Najeriya karɓar uzuri daga wajen Hukumar Zaɓen. Haka wannan zai zubar da ƙimar Najeriya ga ƙasashen Duniya masu saka ido a zaben na Najeriya, kasancewar za'ayi dubin kamar akwai lauje cikin naɗi akan ɗage zaɓen, an shirya hakan ne kawai domin wata manufa ta tabka maguɗin zaɓe. Ɗinbin maƙudan kuɗaɗen da jama'a suka salwantar domin shirin zaɓen sun tashi a banza, haka mafi yawa daga cikin al'umma sun baro wasu sassan jihohin da suke neman na sakawa a bakin salati, sun dawo garuruwansu na asali don yin zaɓen, wanda yanzu haka suke cikin nuna damuwarsu a kan wannan ɗage zaɓen. Wannan dai ya sanya zazzafar muhawara da tsokaci ga masharhanta akan al'amurran yau da kull...

UNITED YOUTH MOVEMENT ASSOCIATION OF ZAMFARA STATE!

Wannan ƙungiyar mai suna a sama! ƙungiya ce wadda anka assasa da zimmar kawo kyakkyawan sauyi mai ma'ana a cikin al'umma, musamman matasa waɗanda sune ƙashin bayan ci gaban kowace al'umma a Duniya. Babu wata ƙasa ko wata al'umma da zata ci gaba matukar ba'a gwama matasa a cikinta ba, kasancewar duk wani babban mutum daga yaro zuwa matashi ya fara. Da sannu wannan ƙungiyar zatayi aiki tuƙuru wajen samar da sauyi mai alfanu a cikin al'ummarta wanda kuma insha Allahu za'ayi na'am da shi. A jiya Asabar 01/12/2018 ne, da misalin ƙarfe 12:01 na rana. Ƙungiyar tayi zamanta na farko a wajen tsohon masallacin Rabi'a dake nan Gusau Babban Birnin Jihar Zamfarar Tarayyar Najeriya. A zaman ƙungiyar na farko ta tattauna akan abubuwa maban-banta daga ciki harda ya za'ayi kungiyar ta kai ga sauran ƙananan Hukumomin da muke da su 14 a cikin wannan jihar ta Zamfara, domin ta samu damar yin aikinta gadan-gadan ba tare da samun wata matsala da kan iya bijirowa ...