Skip to main content

YA KAMATA JAM'IYYUN ADAWA A JIHAR ZAMFARA SU ƘAURACEWA BABBAN ZAƁEN GWAMNONI DA NA 'YAN MAJALISUN JIHA DAKE TAFE




Ko shakka babu; kamar yadda ta bayyana ƙarara a zaɓen da ya gudana na shugaban Ƙasa da na 'yan Majalisun tarayya a ranar 23 ga fabrairun makon da ya gabata, irin yadda anka samu tarin matsaloli wajen yin zaɓen, Jam'iyyar APC mai ƙarfin fada a ji a cikin jihar ta Zamfara ita tayi uwa, tayi makarɓiya a cikin zaɓen, ma'ana dai ina nufin jam'iyyar tayi amfani da karfin ikon da take da shi, wajen cin karanta ba babbaka a dukkanin inda aka gabatar da zaɓen duk da kasancewar ita shugabar zaɓe ta jihar Zamfara ta tabbatar da za'ayi zaɓe mai cike da sahihanci da tsafta wanda kowa zaiyi na'am da shi.


A daidai lokacin da aka wayi garin safiyar zuwa runfunan zaɓe wato ranar Asabar, an samu wasu matsaloli, ta fuskar jinkirin kai kayan zaɓe da wuri, inda wasu rahotannin da muka samu daga wasu jihohin ƙasar nan daban-daban sun dade da fara jefa kuri'unsu, alhali kuma a nan jihar Zamfara ba'a kai kayan zabe ba, duk da tabbacin da hukumar shirya zabe ta ƙasa ta bayar na kammala kai kayan zaben a dukkanin lunguna da sakunan jihar ta Zamfara.


Babbar jam'iyyar APCn a jihar Zamfara ta sauyawa talakawan jihar Zamfara  tunane; irin yadda tayi amfani da maƙuddan kudaden Baitil malin gwamnati, wajen siyen masu kada kuri'a ta hanyar baiwa masu kaɗa kuri'a kudi domin zaben jam'iyyar Apc, kasancewar jam'iyyun Adawa a jihar ta Zamfara basu da isasun kuɗaɗen da zasu baiwa al'umma domin jefa musu ƙuri'u.

Duk da Hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yiwa tattalin arzikin ƙasa Tu'annati wato EFCC, Ta gargaɗi 'yan siyasa da bada kudade a lokacin da ake gabatar da zaɓuɓɓaka, amma hakan baiyi tasiri ba, damin masu ƙudi sunyi amfani da kudade wajen sayen masu kaɗa kuri'a a lunguna da saƙunan jihar Zamfara.


Kasancewar gwamnati ta tara komai, haƙiƙa za tayi amfani da wannan damar wajen yin abinda taga dama. Kamar yadda ya faru a zaben da ya gudana, 'ko shakka babu hakan zai faru a zaɓe mai zuwa', abisa wannan nake ganin kamar zaifi dacewa jam'iyyun Adawa su ƙauracewa zaben, saboda yana tattare da rashin adalci da aringizo!


Muna Addu'a da fatan Alheri. Ya Allah ka kawoma jihar Zamfara zaman lafiya da aminci da kwanciyar hankali da wadata.

Allah ya taimaki jihar Zamfara da al'ummarta da masu yi mata fatan Alheri baki daya.

Nagode


Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...