Skip to main content

UNITED YOUTH MOVEMENT ASSOCIATION OF ZAMFARA STATE!



Wannan ƙungiyar mai suna a sama! ƙungiya ce wadda anka assasa da zimmar kawo kyakkyawan sauyi mai ma'ana a cikin al'umma, musamman matasa waɗanda sune ƙashin bayan ci gaban kowace al'umma a Duniya. Babu wata ƙasa ko wata al'umma da zata ci gaba matukar ba'a gwama matasa a cikinta ba, kasancewar duk wani babban mutum daga yaro zuwa matashi ya fara. Da sannu wannan ƙungiyar zatayi aiki tuƙuru wajen samar da sauyi mai alfanu a cikin al'ummarta wanda kuma insha Allahu za'ayi na'am da shi.


A jiya Asabar 01/12/2018 ne, da misalin ƙarfe 12:01 na rana. Ƙungiyar tayi zamanta na farko a wajen tsohon masallacin Rabi'a dake nan Gusau Babban Birnin Jihar Zamfarar Tarayyar Najeriya. A zaman ƙungiyar na farko ta tattauna akan abubuwa maban-banta daga ciki harda ya za'ayi kungiyar ta kai ga sauran ƙananan Hukumomin da muke da su 14 a cikin wannan jihar ta Zamfara, domin ta samu damar yin aikinta gadan-gadan ba tare da samun wata matsala da kan iya bijirowa daga baya ba.


Kungiyar matasa ce zallah! masu ƙokarin samar da sauyi. Kuma ƙungiya ce mai zaman kanta, babu wata ƙungiya da tayi hadaka da ita, domin yin aiki tare, 'wannan kenan' sannan kungiyar tana matukar neman goyon bayan al'umma a sassan da muke dasu daban-daban domin samun gamsasun shawarwari, domin ci gaban tafiyar!

KAƊAN DAGA CIKIN AYYUKAN KUNGIYAR SUNE;

Samar da zaman lafiya a cikin al'ummar jihar Zamfara.

Magance shaye-shayen miyagun kwayoyi a cikin matasa, haɗi da hana tu'ammali da su.

Kashe zaman banza a cikin matasa haɗi da samar masu da ayyukan yi.

Hana matasa ta'addanci a lokacin siyasa.

Koyar da matasa sana'o'in hannu, haɗi da basu tallafi domin yin sana'ar.

Taimakon matasa masu karatu, a manyan makarantun da muke da su a cikin jiha da kewaye.

Taimakon matasan da bashi ya kaisu a Gidan kaso wato (gidan yari).

Kaɗan kenan daga cikin ayyukan da kungiyar take ƙudurin yi, a yankunan da muke da su duk a faɗin jiha kwata!



Rahoto Daga; Nura Muhammad Mai Apple Gusau, Publicity U-Y-M-A Zamfara State 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.