Skip to main content

UNITED YOUTH MOVEMENT ASSOCIATION OF ZAMFARA STATE!



Wannan ƙungiyar mai suna a sama! ƙungiya ce wadda anka assasa da zimmar kawo kyakkyawan sauyi mai ma'ana a cikin al'umma, musamman matasa waɗanda sune ƙashin bayan ci gaban kowace al'umma a Duniya. Babu wata ƙasa ko wata al'umma da zata ci gaba matukar ba'a gwama matasa a cikinta ba, kasancewar duk wani babban mutum daga yaro zuwa matashi ya fara. Da sannu wannan ƙungiyar zatayi aiki tuƙuru wajen samar da sauyi mai alfanu a cikin al'ummarta wanda kuma insha Allahu za'ayi na'am da shi.


A jiya Asabar 01/12/2018 ne, da misalin ƙarfe 12:01 na rana. Ƙungiyar tayi zamanta na farko a wajen tsohon masallacin Rabi'a dake nan Gusau Babban Birnin Jihar Zamfarar Tarayyar Najeriya. A zaman ƙungiyar na farko ta tattauna akan abubuwa maban-banta daga ciki harda ya za'ayi kungiyar ta kai ga sauran ƙananan Hukumomin da muke da su 14 a cikin wannan jihar ta Zamfara, domin ta samu damar yin aikinta gadan-gadan ba tare da samun wata matsala da kan iya bijirowa daga baya ba.


Kungiyar matasa ce zallah! masu ƙokarin samar da sauyi. Kuma ƙungiya ce mai zaman kanta, babu wata ƙungiya da tayi hadaka da ita, domin yin aiki tare, 'wannan kenan' sannan kungiyar tana matukar neman goyon bayan al'umma a sassan da muke dasu daban-daban domin samun gamsasun shawarwari, domin ci gaban tafiyar!

KAƊAN DAGA CIKIN AYYUKAN KUNGIYAR SUNE;

Samar da zaman lafiya a cikin al'ummar jihar Zamfara.

Magance shaye-shayen miyagun kwayoyi a cikin matasa, haɗi da hana tu'ammali da su.

Kashe zaman banza a cikin matasa haɗi da samar masu da ayyukan yi.

Hana matasa ta'addanci a lokacin siyasa.

Koyar da matasa sana'o'in hannu, haɗi da basu tallafi domin yin sana'ar.

Taimakon matasa masu karatu, a manyan makarantun da muke da su a cikin jiha da kewaye.

Taimakon matasan da bashi ya kaisu a Gidan kaso wato (gidan yari).

Kaɗan kenan daga cikin ayyukan da kungiyar take ƙudurin yi, a yankunan da muke da su duk a faɗin jiha kwata!



Rahoto Daga; Nura Muhammad Mai Apple Gusau, Publicity U-Y-M-A Zamfara State 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM GLOBAL INITIATIVES .... PRESS RELEASE ...

Good day Ladies and Gentlemen of the media.                       In the past few days, we were surprised to learn that few among our Foundation members posted online their official statement of resignation from Labour room cabinet. Despite mixed feelings, Let us start by stating the following: 1. We hereby acknowledge your  contributions to the dynamics of the Labour room. Though, letters were served to each and every appointment/portfolio. Its expected that you write to Labour room Leadership about your intentions rather than addressing it to the general public, but nonetheless, its all for good. 2. The leadership of the labour room global initiatives remain focused, as all those that resigned constitute less than 3% of the entire cabinet. 3. We remain committed to d service to humanity 4. Those outsiders that are not acquainted with the processes of the labour room and genesis of the matter should always endeav...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...