Skip to main content

RASHIN GUDANAR DA ZAƁE MAFI YAWA DAGA CIKIN MUTANE SUN TAFKA BABBAR ASARA!



Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau

Hukuncin da hukumar Zaɓe ta ƙasa mai cin gashin kanta da ɗauka na ɗage babban zaɓen da ake sa ran gudanarsa a yau wani babban ƙalubale ne, sannan babu wani gamsashen madogara ko hujja wanda hukumar zatayi godogo da ita, wanda zaisa har mafi yawa daga cikin mutanen Najeriya karɓar uzuri daga wajen Hukumar Zaɓen.


Haka wannan zai zubar da ƙimar Najeriya ga ƙasashen Duniya masu saka ido a zaben na Najeriya, kasancewar za'ayi dubin kamar akwai lauje cikin naɗi akan ɗage zaɓen, an shirya hakan ne kawai domin wata manufa ta tabka maguɗin zaɓe.

Ɗinbin maƙudan kuɗaɗen da jama'a suka salwantar domin shirin zaɓen sun tashi a banza, haka mafi yawa daga cikin al'umma sun baro wasu sassan jihohin da suke neman na sakawa a bakin salati, sun dawo garuruwansu na asali don yin zaɓen, wanda yanzu haka suke cikin nuna damuwarsu a kan wannan ɗage zaɓen.

Wannan dai ya sanya zazzafar muhawara da tsokaci ga masharhanta akan al'amurran yau da kullum a sassan Najeriya dama ƙasashe ƙetare a fannin siyasa dama Demoƙradayyar Najeriya.

Yanzu sau ukku kenan ana ɗaga babban zaɓen na Najeriya, an dai daga zaɓen a shekara ta 2011 da 2015 da kuma 2019, to sai dai wannan karon abun yafi ciwa mutane tuwo a kwarya, kasancewar dubban mutane sun kwanta bacci ne da niyyar yau su halarci runfunan zaɓen, saidai sun wayi gari da jin an ɗage zaɓen, duk da kalaman hukumar na cewa ta shiryawa zaɓen tun gabanin fara shi a yau, amma abin ya canza salo.

Shugaba Bahari na Najeriya mai mulkin ƙasar a yanzu, kuma mai fafutikar ganin ya ɗare kujerar mulkin a karo na biyu, girmansa da ƙimarsa zai zube ga ƙasashe  duniya, duk da ana masa kallon mutum mai gaskiya.


Da wannan muke kira da babbar murya ga hukumar shirya Zaɓe ta ƙasa da cewa tayi duk mai yiwuwa domin ganin hakan bai sake faruwa ba a nan gaba. Fatan alheri da samun ɗorewar tabbatar da mulkin Demokradiyya a Najeriya.

Daga Nura Mai Apple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...