Skip to main content

RASHIN GUDANAR DA ZAƁE MAFI YAWA DAGA CIKIN MUTANE SUN TAFKA BABBAR ASARA!



Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau

Hukuncin da hukumar Zaɓe ta ƙasa mai cin gashin kanta da ɗauka na ɗage babban zaɓen da ake sa ran gudanarsa a yau wani babban ƙalubale ne, sannan babu wani gamsashen madogara ko hujja wanda hukumar zatayi godogo da ita, wanda zaisa har mafi yawa daga cikin mutanen Najeriya karɓar uzuri daga wajen Hukumar Zaɓen.


Haka wannan zai zubar da ƙimar Najeriya ga ƙasashen Duniya masu saka ido a zaben na Najeriya, kasancewar za'ayi dubin kamar akwai lauje cikin naɗi akan ɗage zaɓen, an shirya hakan ne kawai domin wata manufa ta tabka maguɗin zaɓe.

Ɗinbin maƙudan kuɗaɗen da jama'a suka salwantar domin shirin zaɓen sun tashi a banza, haka mafi yawa daga cikin al'umma sun baro wasu sassan jihohin da suke neman na sakawa a bakin salati, sun dawo garuruwansu na asali don yin zaɓen, wanda yanzu haka suke cikin nuna damuwarsu a kan wannan ɗage zaɓen.

Wannan dai ya sanya zazzafar muhawara da tsokaci ga masharhanta akan al'amurran yau da kullum a sassan Najeriya dama ƙasashe ƙetare a fannin siyasa dama Demoƙradayyar Najeriya.

Yanzu sau ukku kenan ana ɗaga babban zaɓen na Najeriya, an dai daga zaɓen a shekara ta 2011 da 2015 da kuma 2019, to sai dai wannan karon abun yafi ciwa mutane tuwo a kwarya, kasancewar dubban mutane sun kwanta bacci ne da niyyar yau su halarci runfunan zaɓen, saidai sun wayi gari da jin an ɗage zaɓen, duk da kalaman hukumar na cewa ta shiryawa zaɓen tun gabanin fara shi a yau, amma abin ya canza salo.

Shugaba Bahari na Najeriya mai mulkin ƙasar a yanzu, kuma mai fafutikar ganin ya ɗare kujerar mulkin a karo na biyu, girmansa da ƙimarsa zai zube ga ƙasashe  duniya, duk da ana masa kallon mutum mai gaskiya.


Da wannan muke kira da babbar murya ga hukumar shirya Zaɓe ta ƙasa da cewa tayi duk mai yiwuwa domin ganin hakan bai sake faruwa ba a nan gaba. Fatan alheri da samun ɗorewar tabbatar da mulkin Demokradiyya a Najeriya.

Daga Nura Mai Apple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020