Skip to main content

Posts

Cikar Shekara Daya; Gwamna Matawalle a Sikelin Nazari!

Assalamu alaikum, Ranka ya dade barka da warhaka da fatan ana ci gaba da gudanar da mulkin wannan jiha cikin koshin lafiya. Allah ya sa haka. Ranka ya dade Sir, cike da girmamawa nake ta ya ka murnar cikarka shekara daya a kan karagar jagorancin al'ummar jihar Zamfara, ko shakka babu wannan babban abun farin ciki ne da sambarka. Allah ya maka jagora har zuwan wa'adin mulkinka. Ranka ya dade Sir! A nazarce kwanaki 360 da ka share kana jan ragamar jihar nan, ko shakka babu an samu cigaba a wurare da dama, kuma abun Yabawa ne a bisa wannan. Mu mun san cewa; ko da  Allah madaukakin sarki ya baka jagorancin wannan jihar ka sameta ne a hargitse, cikin wani mummunan yanayi marar dadi, musamman ta fuskar tsaro, wanda a lokacin mutumin jihar Zamfara a kullum cikin fargaba yake sakamakon mummunan ta'adin 'yan ta'adda, wadanda suka yi sanadiyar rasa rayukan dubban mutune, hadi da cilastawa dubban mutane barin muhallansu ba cikin shiri ba. Hakika abun sambarka ne, ...

Barka Da Ranar Yara Ta Duniya

kowace shekara majalisar dunkin duniya na ware 27 ga watan 5 domin murnar zagayowar samun 'yancin yara, wannan na zuwa ne la'akari da muhimmancin dake akwai da kuma irin  yadda ya kamata a kula da yara, kasancewar wata rana sune manyan gobe. Ranar ta bana na zawa ne a lokacin da duniya ke cikin firgita da gigitar halin da ta tsintsin kanta a ciki na mummunar annobar cutar korona, a wannan shekarar bukin ba zai samu wani armashi ba, kasancewar har yanzu duniya bata murmure ba akan cutar covid19, wanda ya hallaka dubban mutane a sassa daban-daban na duniya. Ita ma Najeriya ta kan bi sahun takwarorinta wajan gudanar da irin wannan biki a duk shekara, sai dai bana wannan biki ba zai yiyuwa ba, kasancewar wasu daga cikin jihohin ƙasar suna fama da dokar kulle domin kandagarkin hana yaɗuwar cutar korona. Bikin yana tara makarantu da dama inda manyan mutane musamman ma'aikatan gwamnati suke halarta domin kallon faretin girma, inda wasu lokutan akan aza gasa kuma a gabata...

Rayuwa; me nene mararrabar Talaka da bawa a yau

idan muka yi tsinkaye muka bibiyi tarihi da kuma yadda rayuwar bayi ta kasance a shekaru da dama da suka gabata, zamu ga sun sha fama ba kaɗan ba, ta kowane fanni na rayuwa domin ana fataucin mutune kamar yadda mafarauta ke farautar dabbobin daji. Ana kama mutane daga wannan gari zuwa wancen, daga wannan kasa zuwa waccen, domin kaiwa a siyar, kuma aka dauki wannan a matsayin sana'a. A wancen lokaci, idan ka siyo bawa a kasuwa, ya zama mamanlakinka, zaka kaishi a gidanka ne, ko gonarka koma duk inda kake bukatarsa domin yayi maka ayyukan da kake so, ko ya so ko bai so ba, wannan cilas ne a wuyansa. To sai dai duk da haka, shi kuma mamalakin bawan ya zama wajibi a kansa cin sa da shansa kula da lafiyarsa da kuma wajan kwanansa, da tsare masa dukkanin bukatun yau da kullum. Idan masu karatu zasu yi dogon nazari a kan wannan shimfidar zasu fahimce inda na dosa ko da kuwa ban iyar da furta abun da nake son furtawa ba. Idan muka kalli yadda bayi a lokacin mulkin mallaka sun ...

Dokar Kulle; Jinjina ga gwamnatin Jihar Zamfara

tun bayan samun bullar cutar nan mai sarke numfashi ta Covid-19 a jihar Zamfara. A kokarin gwamna Bello Muhammad Mawatallen Maradun, na ganin ya dakile yaduwar cutar a cikin jihar tasa, yake ta shige da ficen ganin gwamman mutane basu harbu da cutara a jihar ba. Gwamna Matawallen ya bullo da wasu sabbin tsare-tsare daga ciki har da jan hankulan al'umma wajan rage tarurukan jama'a barkatai, da kuma bayar da tazara tsakanin mutum da mutum, hadi da samar da sabulun tsaftacce hannuwa, da kuma samar da kayayyakin feshi, wanda alhamdulillahi mun sheda haka, tun lokacin da aka samar da wadannan kayan aiki, mun shedi an nada wani kwamiti mai karfin gaske, wanda ya bazama lunguna da sakuna, ma'aikatai da kuma bankuna, da unguwanni a na gudanar da aikin feshi domin kandagarkin bazuwar annobar cutar Korona mai saurin yaduwa kamar wutar daji. Haka mun shedi irin yadda muka ga an samar da wasu mashuna masu kafa ukku, na daukar marasa lafiya, ga duk wanda aka ga ya nuna alamun ka...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020

Talakawa na buƙatar Tallafi

Kasancewar kowace shekara idan irin wannan lokaci ya kama, malamai hadi da dai-dai kun jama'a suna cigaba da kiraye-kiraye domin tallafawa al'umma musamman masu dankaramin karfi. To babu ko shakka, zamu iya cewa kowace shekara akwai sauki sosai idan muka kamanta ta da shakarar bana, domin kuwa ba talakawan ba har masu kudin suna jin a jikinsu, idan muna dubi yadda komai ya tsaya cik sakamakon cutar annobar korona wanda ta addabi duniya baki daya. Duk da haka, kasancewar sai da ruwan ciki ake janyo na rijiya, akwai bukatar masu hannu da shuni da su dubi girman Allah su taimakawa al'umma, domin ana cikin halin kuncin rayuwa, a bangarori daban-daban na sassan ƙasar nan. Babu yadda za'ayi mu samu cigaba ta kowane fanni sai in ya kasance mun sanya tausayi ga na kasa damu. Tun cen dama Najeriya tana cikin halin matsi tun kafin zuwan wannan lokaci wanda kuma mafi yawa daga cikin al'ummar ƙasar sun san haka, fatan 'yan uwanmu masu hannu da shuni, 'yan kasuwa...

ME MUKA SHIRYA DOMIN TARBON RAMADAN?

Gidauniyar Yazeed Trust Fund ta shirya wani zama na musamman a ofishin kungiyar dake hannun riga da jifatu a karamar hukumar Gusau jihar Zamfara, anyi wannan zaman  ne na taron addu'o'i hadi da nasihohi domin tarbon Azumin watan Ramadan mai falala da albarka. Kafatanin shugabannin mata na wannan tafiyar ne sun ka shirya wannan zama, inda aka gayyato Malama Maryam  'Na-Inna domin ta bayar da tata gudunmuwa ga matan da suka halarci wannan zama. In da malama, tayi muhimman jawabai daga cikin harda tabo muhimmancin dake akwai wajan bayar da taimako musamman ga marayu, haka kuma ta kwadaitar da irin romon dake cikin wannan wata, a wajan Allah madaukakin Sarki. Na inna ta ce; ''Manzon Allah (S.A.W) ya yi nuni da 'yan yatsun hannayensa yace; shi da mai kula da maraya suna zo-zo-zo a cikin al'janna''. Sannan ta kara da cewar; '' tayi  murna. Da irin yadda taga wannan kungiyar mai kokarin taimakon Al'umm, babu ko shakka tayi mamak...