Skip to main content

ME MUKA SHIRYA DOMIN TARBON RAMADAN?




Gidauniyar Yazeed Trust Fund ta shirya wani zama na musamman a ofishin kungiyar dake hannun riga da jifatu a karamar hukumar Gusau jihar Zamfara, anyi wannan zaman  ne na taron addu'o'i hadi da nasihohi domin tarbon Azumin watan Ramadan mai falala da albarka.

Kafatanin shugabannin mata na wannan tafiyar ne sun ka shirya wannan zama, inda aka gayyato Malama Maryam  'Na-Inna domin ta bayar da tata gudunmuwa ga matan da suka halarci wannan zama. In da malama, tayi muhimman jawabai daga cikin harda tabo muhimmancin dake akwai wajan bayar da taimako musamman ga marayu, haka kuma ta kwadaitar da irin romon dake cikin wannan wata, a wajan Allah madaukakin Sarki.

Na inna ta ce; ''Manzon Allah (S.A.W) ya yi nuni da 'yan yatsun hannayensa yace; shi da mai kula da maraya suna zo-zo-zo a cikin al'janna''.

Sannan ta kara da cewar; '' tayi  murna. Da irin yadda taga wannan kungiyar mai kokarin taimakon Al'umm, babu ko shakka tayi mamakin ace ba'a samun ire-irin wadannan kungiyoyi a cikin unguwanni, domin taimakon al'umma musamman masu dan karamin karfi''.


Watan Ramadan wata ne mai falala wanda Allah madaukakin sarki yake lunka rahama da jinkai ga bayinsa, ko shakka babu yana da kyau mu kara rubanya kokarinmu wajan taimakon 'yan uwa masu dan karamin karfi a cikin al'umma domin rage masu radadin rayuwa.


A cikin jawabinta. Shugaban kwamitin mata, ta Gidauniyar (Alh, Yazeed Shehu Danfulani, garkuwan Matasan Gusau, Lamidon Tsafe) wato Hajiya Maryam Danfuloti tayi jawabin godiya, ga dukkan ilahirin al'ummar da sunka samu damar halartar wannan taro, sannan tayi godiya, ga Malama Maryam a bisa karba goron gayyata na zuwa wannan wajan, tare da bayar da tata gudunmuwa wajan ciyar da al'umma a gaba.


Malama Maryam Na Inna. Malama ce wadda ta shahara wajan koyar da al'umma tarbiyya da kuma sanin ya kamata,, muna fatan Allah ya saka mata da mafificin alheri, ya yiwa zuri'arta albarka.

A nasa jawabin, jagoran tafiyar Gidauniyar Yazeed Trust Fund, (Comrade Rufa'i Bala UB Gusau, shima yayi jinjina da yabo ga dukkan al'ummar da sunka samu damar halartar wannan muhimmin zama da ya gudana. Haka shima kansa yayi tsokaci akan manufar Gidauniyar wajan Daukar nauyin yara marayu zuwa makaranta hadi da dauke masu dukkan wahalhalun rayuwa, inda yace yanzu haka wannan shiri mai taken ''Yara Masu Daraja'' ya nan kuna yana cigaba da yin dubon tsanaki a cikin al'umma, domin zakulo masu dan karamin karfi a cikin al'umma don dauke masu nauyin karatu, tare da kula lafiyarsu.

Haka a ci gaban jawaban na mutane daban-daban a wajan, sun tabo maganar cutar nan mai matukar hatsari a cikin al'umma, kuma mai saurin yaduwa ta Covid19, da kuma hanyoyin da ya kamata al'umma subi wajan kare kansu da kamuwa da wannan cuta, kasancewar hausawa suna cewa Riga Kafi Yafi Magani.

A karshe anyi addu'o'i na musamman na samun zaman lafiya madauwami a jihar Zamfara da Najeriya baki daya

Nura Mai Apple Media Reporter daga Gusau

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.