Skip to main content

ME MUKA SHIRYA DOMIN TARBON RAMADAN?




Gidauniyar Yazeed Trust Fund ta shirya wani zama na musamman a ofishin kungiyar dake hannun riga da jifatu a karamar hukumar Gusau jihar Zamfara, anyi wannan zaman  ne na taron addu'o'i hadi da nasihohi domin tarbon Azumin watan Ramadan mai falala da albarka.

Kafatanin shugabannin mata na wannan tafiyar ne sun ka shirya wannan zama, inda aka gayyato Malama Maryam  'Na-Inna domin ta bayar da tata gudunmuwa ga matan da suka halarci wannan zama. In da malama, tayi muhimman jawabai daga cikin harda tabo muhimmancin dake akwai wajan bayar da taimako musamman ga marayu, haka kuma ta kwadaitar da irin romon dake cikin wannan wata, a wajan Allah madaukakin Sarki.

Na inna ta ce; ''Manzon Allah (S.A.W) ya yi nuni da 'yan yatsun hannayensa yace; shi da mai kula da maraya suna zo-zo-zo a cikin al'janna''.

Sannan ta kara da cewar; '' tayi  murna. Da irin yadda taga wannan kungiyar mai kokarin taimakon Al'umm, babu ko shakka tayi mamakin ace ba'a samun ire-irin wadannan kungiyoyi a cikin unguwanni, domin taimakon al'umma musamman masu dan karamin karfi''.


Watan Ramadan wata ne mai falala wanda Allah madaukakin sarki yake lunka rahama da jinkai ga bayinsa, ko shakka babu yana da kyau mu kara rubanya kokarinmu wajan taimakon 'yan uwa masu dan karamin karfi a cikin al'umma domin rage masu radadin rayuwa.


A cikin jawabinta. Shugaban kwamitin mata, ta Gidauniyar (Alh, Yazeed Shehu Danfulani, garkuwan Matasan Gusau, Lamidon Tsafe) wato Hajiya Maryam Danfuloti tayi jawabin godiya, ga dukkan ilahirin al'ummar da sunka samu damar halartar wannan taro, sannan tayi godiya, ga Malama Maryam a bisa karba goron gayyata na zuwa wannan wajan, tare da bayar da tata gudunmuwa wajan ciyar da al'umma a gaba.


Malama Maryam Na Inna. Malama ce wadda ta shahara wajan koyar da al'umma tarbiyya da kuma sanin ya kamata,, muna fatan Allah ya saka mata da mafificin alheri, ya yiwa zuri'arta albarka.

A nasa jawabin, jagoran tafiyar Gidauniyar Yazeed Trust Fund, (Comrade Rufa'i Bala UB Gusau, shima yayi jinjina da yabo ga dukkan al'ummar da sunka samu damar halartar wannan muhimmin zama da ya gudana. Haka shima kansa yayi tsokaci akan manufar Gidauniyar wajan Daukar nauyin yara marayu zuwa makaranta hadi da dauke masu dukkan wahalhalun rayuwa, inda yace yanzu haka wannan shiri mai taken ''Yara Masu Daraja'' ya nan kuna yana cigaba da yin dubon tsanaki a cikin al'umma, domin zakulo masu dan karamin karfi a cikin al'umma don dauke masu nauyin karatu, tare da kula lafiyarsu.

Haka a ci gaban jawaban na mutane daban-daban a wajan, sun tabo maganar cutar nan mai matukar hatsari a cikin al'umma, kuma mai saurin yaduwa ta Covid19, da kuma hanyoyin da ya kamata al'umma subi wajan kare kansu da kamuwa da wannan cuta, kasancewar hausawa suna cewa Riga Kafi Yafi Magani.

A karshe anyi addu'o'i na musamman na samun zaman lafiya madauwami a jihar Zamfara da Najeriya baki daya

Nura Mai Apple Media Reporter daga Gusau

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020