Skip to main content

Talakawa na buƙatar Tallafi



Kasancewar kowace shekara idan irin wannan lokaci ya kama, malamai hadi da dai-dai kun jama'a suna cigaba da kiraye-kiraye domin tallafawa al'umma musamman masu dankaramin karfi. To babu ko shakka, zamu iya cewa kowace shekara akwai sauki sosai idan muka kamanta ta da shakarar bana, domin kuwa ba talakawan ba har masu kudin suna jin a jikinsu, idan muna dubi yadda komai ya tsaya cik sakamakon cutar annobar korona wanda ta addabi duniya baki daya.

Duk da haka, kasancewar sai da ruwan ciki ake janyo na rijiya, akwai bukatar masu hannu da shuni da su dubi girman Allah su taimakawa al'umma, domin ana cikin halin kuncin rayuwa, a bangarori daban-daban na sassan ƙasar nan.

Babu yadda za'ayi mu samu cigaba ta kowane fanni sai in ya kasance mun sanya tausayi ga na kasa damu. Tun cen dama Najeriya tana cikin halin matsi tun kafin zuwan wannan lokaci wanda kuma mafi yawa daga cikin al'ummar ƙasar sun san haka, fatan 'yan uwanmu masu hannu da shuni, 'yan kasuwa da ma'aikatan gwamnati zasu taimakawa al'umma daidai gwargwadon hali, kasancewar wannan wata ne mai matukar tarin lada,

muna roko ga gwamnatocinmu na jihohi musamman wadanda suka kakaba dokar zama a gida domin hanawa tare da dakile yaduwar annobar Korona, su dubi halin da al'umma ke ciki, su fitar da wani kaso na musamman wanda za a rika bi ana tallafawa talakawa na cikin birane da karkara, hakan zai taimaka wajan rage radadin zaman rashi dake addabar al'umma musamman marasa galihu.


Haka muna kira ga gwamnatin tarayyar Najeriya karkashin jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari, ya dubi sauran takwarorinsa na wasu kasashe, inda suke bada gagarumar gudunmuwa ga talakawansu, domin rage masu halin da suke ciki na zama a gida, shima ya tallafa ma 'yan kasansa, sannan abi tsari mai kyau wanda tallafi zai iya kaiwa ga wadanda akayi dominsu.

Muna fatan Allah ya kawo mana ƙarshen wannan cuta, kuma ya bada ikon tallafama al'umma, Allah ya karo arziki mai albarka a Najeriya da Afrika da ma duniya baki daya.

Ramadan Mukarram.

Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020



Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.