Skip to main content

Rayuwa; me nene mararrabar Talaka da bawa a yau



idan muka yi tsinkaye muka bibiyi tarihi da kuma yadda rayuwar bayi ta kasance a shekaru da dama da suka gabata, zamu ga sun sha fama ba kaɗan ba, ta kowane fanni na rayuwa domin ana fataucin mutune kamar yadda mafarauta ke farautar dabbobin daji. Ana kama mutane daga wannan gari zuwa wancen, daga wannan kasa zuwa waccen, domin kaiwa a siyar, kuma aka dauki wannan a matsayin sana'a.

A wancen lokaci, idan ka siyo bawa a kasuwa, ya zama mamanlakinka, zaka kaishi a gidanka ne, ko gonarka koma duk inda kake bukatarsa domin yayi maka ayyukan da kake so, ko ya so ko bai so ba, wannan cilas ne a wuyansa.

To sai dai duk da haka, shi kuma mamalakin bawan ya zama wajibi a kansa cin sa da shansa kula da lafiyarsa da kuma wajan kwanansa, da tsare masa dukkanin bukatun yau da kullum.

Idan masu karatu zasu yi dogon nazari a kan wannan shimfidar zasu fahimce inda na dosa ko da kuwa ban iyar da furta abun da nake son furtawa ba.


Idan muka kalli yadda bayi a lokacin mulkin mallaka sun kayi rayuwa. Idan muka kalli yadda talakan Najeriya ke rayuwa a yau zasu dau wasu darusa masu matukar yawa.

Kamar; idan mukayi la'akari da yadda 'yan siyasa ke amfani da halsunansu wajan alkhawulla tare da yin dadin baki a duk lokacin da suke neman al'umma ido rufe, babu ko shakka abun ban tsoro ne. 'yan siyasa sun san lunguna da sakunan kauyuka da birane a lokacin yakin neman zabe, amma abunda ke ba jama'a mamaki shine yadda suke ɓacewa ɓat da zarar sun kai ga madafun iko.

A lokacin ne zasu fitar da dukkan tsare-tsaren da sun ka ga dama, wanda ya masu dadi, domin a lokacin da suka kai inda suke harare, suna sanya dukkan wani tsari wanda yayi daidai da muradunsu, ko da kuwa hakan zai jefa gwamman al'umma cikin halin ni-'ya'su.

A wannan zamani an mayar da rayuwar talaka ba a bakin komai ba, idan muka kalli yadda ake cigaba da kakabawa jama'a dokar kulle ba tare an samar masu da muhimman abubuwan da zasuyi amfani da su na yau da kullum ba, kasancewar ana tsoron kamuwa da cutar Korona mai saurin yaɗuwa, to amma kuma ba'ayi nazarin sakamakon haka mutane masu matukar yawa zasu iya kamuwa da cutar yunwa ba.

Idan muka kalli bayanin masana a sha'anin kiyon lafiya, sun tabbatar da mutum zai iya kamuwa da cutar Korona har ya warke ba tare da shi kanshi ya san ya kamu da cutar ba. To wannan kuma ya sha bamban da cutar yunwa, domin ita kan bayyana kuma ta aika mutum barzahu ba tare da bata lokaci ba.

Wani abu da ake yiwa talaka mai kama da kisan mummuke, a buge shi kuma a hanashi kuka, babu ko shakka ba za a samu cigaba ba har sai an samar da gyara.

Gyaran kuwa  a dauki al'umma a matsayin bai daya, sannan shugabanni suyi adalci ga talakawa, sannan su san abun tambaya ne a kan irin jagorancin da Allah madaukakin sarki ya basu. Su kuma talakawa wajibi ne su kasance masu nuna da'a da biyayya tare da barin la'antar shugabanni, wannan kawai ce hanyar da za'a bi domin ganin an samar da al'umma managarciyya abar alfahari.

Muna fatan Allah ya sanya tausayin shugabanni ga talakawa, mu kuma Allah ya bamu ikon yi masu biyayya daidai gwargwado. A ƙarshe muna Addu'ar Allah ya bamu lafiya da zama a Najeriya Afrika da ma duniya baki daya.

Daga Nura Mai Apple Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...