Skip to main content

Rayuwa; me nene mararrabar Talaka da bawa a yau



idan muka yi tsinkaye muka bibiyi tarihi da kuma yadda rayuwar bayi ta kasance a shekaru da dama da suka gabata, zamu ga sun sha fama ba kaɗan ba, ta kowane fanni na rayuwa domin ana fataucin mutune kamar yadda mafarauta ke farautar dabbobin daji. Ana kama mutane daga wannan gari zuwa wancen, daga wannan kasa zuwa waccen, domin kaiwa a siyar, kuma aka dauki wannan a matsayin sana'a.

A wancen lokaci, idan ka siyo bawa a kasuwa, ya zama mamanlakinka, zaka kaishi a gidanka ne, ko gonarka koma duk inda kake bukatarsa domin yayi maka ayyukan da kake so, ko ya so ko bai so ba, wannan cilas ne a wuyansa.

To sai dai duk da haka, shi kuma mamalakin bawan ya zama wajibi a kansa cin sa da shansa kula da lafiyarsa da kuma wajan kwanansa, da tsare masa dukkanin bukatun yau da kullum.

Idan masu karatu zasu yi dogon nazari a kan wannan shimfidar zasu fahimce inda na dosa ko da kuwa ban iyar da furta abun da nake son furtawa ba.


Idan muka kalli yadda bayi a lokacin mulkin mallaka sun kayi rayuwa. Idan muka kalli yadda talakan Najeriya ke rayuwa a yau zasu dau wasu darusa masu matukar yawa.

Kamar; idan mukayi la'akari da yadda 'yan siyasa ke amfani da halsunansu wajan alkhawulla tare da yin dadin baki a duk lokacin da suke neman al'umma ido rufe, babu ko shakka abun ban tsoro ne. 'yan siyasa sun san lunguna da sakunan kauyuka da birane a lokacin yakin neman zabe, amma abunda ke ba jama'a mamaki shine yadda suke ɓacewa ɓat da zarar sun kai ga madafun iko.

A lokacin ne zasu fitar da dukkan tsare-tsaren da sun ka ga dama, wanda ya masu dadi, domin a lokacin da suka kai inda suke harare, suna sanya dukkan wani tsari wanda yayi daidai da muradunsu, ko da kuwa hakan zai jefa gwamman al'umma cikin halin ni-'ya'su.

A wannan zamani an mayar da rayuwar talaka ba a bakin komai ba, idan muka kalli yadda ake cigaba da kakabawa jama'a dokar kulle ba tare an samar masu da muhimman abubuwan da zasuyi amfani da su na yau da kullum ba, kasancewar ana tsoron kamuwa da cutar Korona mai saurin yaɗuwa, to amma kuma ba'ayi nazarin sakamakon haka mutane masu matukar yawa zasu iya kamuwa da cutar yunwa ba.

Idan muka kalli bayanin masana a sha'anin kiyon lafiya, sun tabbatar da mutum zai iya kamuwa da cutar Korona har ya warke ba tare da shi kanshi ya san ya kamu da cutar ba. To wannan kuma ya sha bamban da cutar yunwa, domin ita kan bayyana kuma ta aika mutum barzahu ba tare da bata lokaci ba.

Wani abu da ake yiwa talaka mai kama da kisan mummuke, a buge shi kuma a hanashi kuka, babu ko shakka ba za a samu cigaba ba har sai an samar da gyara.

Gyaran kuwa  a dauki al'umma a matsayin bai daya, sannan shugabanni suyi adalci ga talakawa, sannan su san abun tambaya ne a kan irin jagorancin da Allah madaukakin sarki ya basu. Su kuma talakawa wajibi ne su kasance masu nuna da'a da biyayya tare da barin la'antar shugabanni, wannan kawai ce hanyar da za'a bi domin ganin an samar da al'umma managarciyya abar alfahari.

Muna fatan Allah ya sanya tausayin shugabanni ga talakawa, mu kuma Allah ya bamu ikon yi masu biyayya daidai gwargwado. A ƙarshe muna Addu'ar Allah ya bamu lafiya da zama a Najeriya Afrika da ma duniya baki daya.

Daga Nura Mai Apple Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020