Skip to main content

Dokar Kulle; Jinjina ga gwamnatin Jihar Zamfara



tun bayan samun bullar cutar nan mai sarke numfashi ta Covid-19 a jihar Zamfara. A kokarin gwamna Bello Muhammad Mawatallen Maradun, na ganin ya dakile yaduwar cutar a cikin jihar tasa, yake ta shige da ficen ganin gwamman mutane basu harbu da cutara a jihar ba.

Gwamna Matawallen ya bullo da wasu sabbin tsare-tsare daga ciki har da jan hankulan al'umma wajan rage tarurukan jama'a barkatai, da kuma bayar da tazara tsakanin mutum da mutum, hadi da samar da sabulun tsaftacce hannuwa, da kuma samar da kayayyakin feshi, wanda alhamdulillahi mun sheda haka, tun lokacin da aka samar da wadannan kayan aiki, mun shedi an nada wani kwamiti mai karfin gaske, wanda ya bazama lunguna da sakuna, ma'aikatai da kuma bankuna, da unguwanni a na gudanar da aikin feshi domin kandagarkin bazuwar annobar cutar Korona mai saurin yaduwa kamar wutar daji.

Haka mun shedi irin yadda muka ga an samar da wasu mashuna masu kafa ukku, na daukar marasa lafiya, ga duk wanda aka ga ya nuna alamun kamuwa da cutar ta korona da dangoginta, hadi da wayar da kan al'umma a kan hadarin da ke tattare da wannan cuta, domin al'umma suyi taka tsan-tsan, ko shakka babu abun yabawa ne, kuma  abun farin ciki ne da sambarka.

Kasancewar jihar Zamfara tana daga cikin jerin jahohin  arewacin Najeriya da al'ummarta  ke fama da radadin talauci. Mafi yawa daga cikin al'ummar jihar sun nuna takaicinsu a lokacin da gwamnan ya fito ya aiyana dokar takaita gudanar da sallar jam'i tare da dakatar da sallar juma'a a duk fadin jihar ta Zamfara, baya ga dokar gwamnatin tarayya wanda ta saka a duk fadin kasar na sanya dokar hana fita tun daga karfe 8 na dare zuwa 6 na asuba. Mutane da dama sun koka sosai kasancewar kaso mai yawa sai sun fito sun nema kafin zuwa a girka abinci a gida.

Mutane da dama sun nuna bacin ransu  a kan wannan mataki. Gwamna Matawalle ya sanya dokar ne na takaita sallar jam'i na tsawon mako daya, sai dai wani babban abun farin ciki shine, bayan kammala makon, gwamnan ya fito yayi jawabin janye dokar hadi da yiwa al'ummar jihar gamsashen bayani akan wannan mataki da kuma dalilin daukarsa.

Ko shakka babu irin yadda gwamnan yayi saurin janje wannan doka ya sanya farin cikin a cikin zuciyoyin talakawan jihar, kasancewar kaso mai yawa daga cikin al'ummar jihar musulmai ne.


Godiya ta musamman ga gwamna Bello Muhammad Matawalle akan kokarinsa wajan ganin ya kamata adalci da gaskiya a cikin mulkinsa, muna fatan hakan zai cigaba da dorewa.

Muna kira ga sauran kafatanin gwamnonin da suka sanya dokar kulle domin takaita yaduwar cutar Korona, zasu dubi talakawansu da idon rahama su tausaya masu, in har dole ne sai dokar tayi aiki, to a fitar da tsari mai kyau da bayar da wani abu ga talakawa domin rage masu radadin abunda ke da mun su.

Fatan alheri ga gwamnatin jihar Zamfara da makarabanta masu kokarin ganin an kamanta gaskiya da adalci a tsakanin al'umma.

Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

KUNGIYAR MURYAR TALAKA TA BAYAR DA TALLAFIN KAYAN MAKARANTA, GA DALIBBAI DA KADDAMAR DA SHUWAGABANNINTA A KARAMAR HUKUMAR MARU!

A yau Talata 19-12-2017 kungiyar Muryar Talaka ta kasa Reshen Jahar Zamfara. Kai ziyara a Karamar hukumar Maru domin bayar da tallafin kayan karatu ga dalibbai a makarantun Gwamnati da ke wadannan karamar hukumar . A lokacin ziyarar wadda shugaban kungiyar na Jahar Zamfara, Comrade HAFIZU BALARABE GUSAU. ya jagoranta. Ya bayyana cewa, kungiyar Muryar Talaka ta bullo da wannan shirin ne, domin tallafawa, wajen cigaban bangaren ilimi a wannan jahar. Wanda hakan ne, ya sa kungiyar ta bullo da wannan shirin La'akkari da yadda wasu uwaye su ke da matukar rauni wajen daukar nauyin dawainiyar 'ya'yansu. Haka zalika hakan zai taimaka wajen habbaka sha'anin ILIMI a Jahar Zamfara. A lokacin da ya ke jawabi shugaban makarantar BANAGA SULE Primary school, Maru. Ya bayyana kungiyar muryar Talaka da cewa "Kungiya ce da ya kamata sauran kungiyoyi su yi koyi da ita. "Dan Haka ya kamata ku Kara jajircewa wajen aiki tukuru. Musamman ganin cewa kungiyar, ba kungiya ba ...