Skip to main content

Dokar Kulle; Jinjina ga gwamnatin Jihar Zamfara



tun bayan samun bullar cutar nan mai sarke numfashi ta Covid-19 a jihar Zamfara. A kokarin gwamna Bello Muhammad Mawatallen Maradun, na ganin ya dakile yaduwar cutar a cikin jihar tasa, yake ta shige da ficen ganin gwamman mutane basu harbu da cutara a jihar ba.

Gwamna Matawallen ya bullo da wasu sabbin tsare-tsare daga ciki har da jan hankulan al'umma wajan rage tarurukan jama'a barkatai, da kuma bayar da tazara tsakanin mutum da mutum, hadi da samar da sabulun tsaftacce hannuwa, da kuma samar da kayayyakin feshi, wanda alhamdulillahi mun sheda haka, tun lokacin da aka samar da wadannan kayan aiki, mun shedi an nada wani kwamiti mai karfin gaske, wanda ya bazama lunguna da sakuna, ma'aikatai da kuma bankuna, da unguwanni a na gudanar da aikin feshi domin kandagarkin bazuwar annobar cutar Korona mai saurin yaduwa kamar wutar daji.

Haka mun shedi irin yadda muka ga an samar da wasu mashuna masu kafa ukku, na daukar marasa lafiya, ga duk wanda aka ga ya nuna alamun kamuwa da cutar ta korona da dangoginta, hadi da wayar da kan al'umma a kan hadarin da ke tattare da wannan cuta, domin al'umma suyi taka tsan-tsan, ko shakka babu abun yabawa ne, kuma  abun farin ciki ne da sambarka.

Kasancewar jihar Zamfara tana daga cikin jerin jahohin  arewacin Najeriya da al'ummarta  ke fama da radadin talauci. Mafi yawa daga cikin al'ummar jihar sun nuna takaicinsu a lokacin da gwamnan ya fito ya aiyana dokar takaita gudanar da sallar jam'i tare da dakatar da sallar juma'a a duk fadin jihar ta Zamfara, baya ga dokar gwamnatin tarayya wanda ta saka a duk fadin kasar na sanya dokar hana fita tun daga karfe 8 na dare zuwa 6 na asuba. Mutane da dama sun koka sosai kasancewar kaso mai yawa sai sun fito sun nema kafin zuwa a girka abinci a gida.

Mutane da dama sun nuna bacin ransu  a kan wannan mataki. Gwamna Matawalle ya sanya dokar ne na takaita sallar jam'i na tsawon mako daya, sai dai wani babban abun farin ciki shine, bayan kammala makon, gwamnan ya fito yayi jawabin janye dokar hadi da yiwa al'ummar jihar gamsashen bayani akan wannan mataki da kuma dalilin daukarsa.

Ko shakka babu irin yadda gwamnan yayi saurin janje wannan doka ya sanya farin cikin a cikin zuciyoyin talakawan jihar, kasancewar kaso mai yawa daga cikin al'ummar jihar musulmai ne.


Godiya ta musamman ga gwamna Bello Muhammad Matawalle akan kokarinsa wajan ganin ya kamata adalci da gaskiya a cikin mulkinsa, muna fatan hakan zai cigaba da dorewa.

Muna kira ga sauran kafatanin gwamnonin da suka sanya dokar kulle domin takaita yaduwar cutar Korona, zasu dubi talakawansu da idon rahama su tausaya masu, in har dole ne sai dokar tayi aiki, to a fitar da tsari mai kyau da bayar da wani abu ga talakawa domin rage masu radadin abunda ke da mun su.

Fatan alheri ga gwamnatin jihar Zamfara da makarabanta masu kokarin ganin an kamanta gaskiya da adalci a tsakanin al'umma.

Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020