Skip to main content

Posts

Gwamnatin tarayya ta yi watsi da kudirin samar wa makiyaya filayen kiwo a jihohi

Gwamnatin tarayya ta ba kowace jiha damar daukan matakin da zai kawo karshen rikicin makiyaya a kasar Gwamnatin tarayya ta yi watsi da kudirin samar wa makiyaya filayen kiwo a jihohi Kwamitin mutane 10 da majalissar zartarwa ta kafa dan kawo karshen hare-haren makiyaya wasu sassan kasar, ta ba kowace jiha damar daukan matakin da take ganin zai kawo karshen matsalar. Kwamitin wanda mataimakin shugaban kasa, Ferfesa Yemi Osinbanjo yake jagoranta, ya hadda da gwamnonin jihar Zamfara, Kaduna, Adamawa, Benuwe, Filato, Ebonyi da Oyo. Wani babban jami’in fadar shugaban kasa ya fadawa manema labaru a ranar Lahadi cewa, gwamnatin tarayya bata son ta tilasatawa jihohi yin abubuwan da basa son yi. Gwamnatin tarayya ta yi watsi da kudirin samar wa makiyaya filayen kiwo a jihohi Yace mataikamakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo, ya bayyana haka wani taro da suka yi. Jami’in wanda baya son a bayyana sunan shi yace, mataimakin shugaban kasa ya lura da irin fargaban da wasu jihohi suk...

Buhari ya rattaba hannu a kan dokar ƙara wa ‘yan majalisu ƙarfin iko a kasar nan

Buhari ya rattaba hannu a kan dokar ƙara wa ‘yan majalisu ƙarfin iko a kasar nan A ranar Juma’ar da ta gabata ne, shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya rattaba hannu akan wata sabuwar doka ta ƙara wa ‘yan majalisu ƙarfin iko a kasar nan. Wannan doka ta baiwa ‘yan majalisun tarayya da kuma na jihohi wata dama ta kare su daga duk wani laifukan furuci da suka aikata, inda ta kuma faɗaɗa ikonsu na umartar jami’ai wajen cafke duk wani da ya saɓawa dokokin su. Shugaban kasa; Muhammadu Buhari majiyar Mai Apple, ta kuma fahimci cewa, dokar ta bayar da iko ga ‘yan majalisu na kiranyen duk wani mutum ya gurfana a gaban su domin bayar da wata shaida akan kowane bincike da suke gudanarwa. Jaridar Daily Trust ta ruwaito da sanadin hadimin shugaban ƙasa akan harkokin majalisun tarayya, Sanata Ita Enang, inda ya bayyana cewa shugaban ya kuma rattaba hannu a kan wasu sabbin dokoki bakwai da ‘yan majalisun su ka buƙata. A ranar da ta gabata ne kuma, Majiyar Mai Apple, ta ruwaito cewa, shugaba ...

Gwamnan Kaduna zai kori masu gadi da ‘yan sako marasa takardun Makaranta daga aiki

Kawo yanzu haka Gwamnatin Jihar Kaduna na cigaba da sallamar Ma’aikatan Jihar da dama. A baya dai Gwamna Malam Nasir El-Rufai ya sallami Malaman Makaranta rututu har 21,780 da kuma Ma’aikatan kananan Hukumomin Jihar. Yanzu kuma dai Gwamnatin Jihar ta Kaduna ta shirya korar masu gadi da ‘yan sako watau masinjoji daga aiki. Gwamnan ya bada umarni cewa ayi waje da duk Ma’aikacin da ya zarce fiye da shekaru 10 yana aiki bai da takarda akalla difloma. Gwamna El-Rufai dai yana ta kokarin kawo gyara a harkar aikin Gwamnati inda yake sassabe Ma’aikata. Kwanakin baya ma dai ya shiga Hukumomi da Makarantun Gwamnatin Jihar ban da kuma Ma’aikatan Masarautu da ya kora a baya. Idan ba ku manta ba kwanan nan wani Dattijo da aka sallama da ke aikin Masinja a Sabon-Gari Zaria ya fadi war-was. A da dai an yi tunani ya rasu amma majiyar mu ta bayyana mana cewa doguwar suma ce kurum tsohon Ma’aikacin yayi.

Hukumar raya birnin Abuja za ta rushe wasu gine-gine 750

Hukumar raya birnin tarayya Abuja (FCTA) ta ce za ta rushe a kalla wasu gine-gine kimanin 750 a unguwar Lugbe domin kiyaye mazauna wurin fadawa cikin hatsari. Darekta a hukumar, Mista Mukhtar Usman Galadima, ya sanar da haka yayin ziyarar yankin gine-ginen da abin zai shafa, yana mai bayyana cewar dukkan gine-ginen basu samu sahalewar hukumar ba kafin a gina su. Galadima ya bayyana cewar anyi gine-ginen ne a karkashin babban layin wutar lantarki, kuma za’a rushe su domin bawa kamfanin raba hasken wutar lantarki sararin yin aiki da kuma kiyaye afkuwar hatsari. ” Nisan da hukuma ta yarda da shi tsakanin kowanne irin gini da babban layin wutar lantarki shine mita 30 ,” a cewar Galadima. Gine-gine dake Unguwannin Tudunwada da Peace Village ne rusau din zai fi shafa. Ko a kwanakin baya saida ministan aiyuka, gidaje, da lantarki, Babatunde Raji Fashola, ya ce gwamnatin tarayya za ta rushe duk wasu gine-gine da aka yi a karkashin babban layin wutar lantarki da kuma wadanda aka yi...

Za a sauya mattatun da Shugaban Kasa ya ba mukami kwanaki

Yanzu haka dai mun ji cewa Fadar Shugaban Kasa za ta sauya mattatun da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ba mukami a Gwamnatin sa kwanaki wanda hakan ya jawo abin maganar ira_iransu. Mai magana da bakin Shugaban Kasar watau Mal. Garba Shehu ya tabbatar da cewa za sake yi wa mukaman da aka bada kwanaki wani kallo inda za a cire sunayen wadanda su ka rasu a maye gurbin su da wasu dabam kwanan nan. Garba Shehu yace za kuma a cire sunayen wadanda yanzu haka sun bar Jam’iyyar APC amma an sa sunan su a mukaman da aka bada kwanaki. Garba Shehu ya bayyanawa Jaridar Punch wannan ne a wayar tarho da su kayi. Daga cikin wadanda aka ba mukaman akwai wasu da su ka rasu tuni, wasu kuma dai sun bar APC zuwa wasu Jam’iyyun adawar. A cikin wadanda Gwamnatin Tarayya ta ba mukaman har da na kusa da Atiku Abubakar da ya koma PDP.

Matsalar Mai: Kungiyar ‘Yan Jarida A Jahar Barno Ta Zargi Jami'an Mai

Kodayake matsalar mai ta fara lafawa a wasu sassan arewacin Najeriya, ganin yadda matsalar ta dada rikita al’amura a arewa maso gabashin Najeriya, musamman ma jahar Barno, Kungiyar ‘Yan Jarida (NUJ), shiyyar jahar ta daga yatsa ma manyan ma’aikatan bangaren man fetur, wadanda ta zarge da barin wasu masu zalama da haddasa matsalar. Bayan yankin arewa maso gabashin Najeriya ya sha fama da karancin da kuma tsadar mai, musamman ma wanda aka yi kwanan nan, Kungiyar ‘Yan Jaridar Najeriya Shiyyar jahar ta Barno ta zargi manyan ma’aikatan bangaren main a Najeriya da rashin tabukawa sosai wajen dakile matsalar. Kungiyar ta yi nuni da yadda Mataimakin Shugaban Najeriya Furfesa Yomi Osunbajo ya yi ta kai koma wajen ganin matsalar ta kau. Kungiyar ta ce sam manyan ma’aikatan bangaren mai bas u taimakawa kuma sun bar wasu manyan ‘yan kasuwa na cin karensu ba babbaka. Da yake karin haske ma wakilinmu a jahar Barno, Haruna Dauda, Shugaban kungiyar ‘yan jaridar, Shiyyar jahar Barno, ...

2019: Buhari ya nada Amaechi darektan Kamfen din sa

Rahotanni sun kawo cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada ministan sufuri, Rotimi Ameachi a matsayin shugaban kamfen din sa a zaben 2019. Wannan shine karo na biyu da shugaban kasar ke daura shi akan wannan mataki. Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa Amaechi ya karbi wasikar nada shi daga fadar shugaban kasa kuma zai sanar wa duniya a mako mai zuwa. A cewar jaridar, bincike da ta gudanar na musamman domin sanin tabbacin wannan rahota ya nuna mata cewa akwai kamshin gaskiya a maganar. Kaduna yayinda Buhari zai ziyarci jihar Majiyar tamu ta ce kakakin Amaechi, David Iyofor, ya shaida mata cewa ba zai iya cewa ehhh ba, kuma ba zai ce a’a ba. Ba tun a yau bane shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ke nuna alamun cewa zai fito takara a 2019. Ya fadi wani abu mai kama da haka da ya ziyar ci mutanen jihar Kano.