Skip to main content

Matsalar Mai: Kungiyar ‘Yan Jarida A Jahar Barno Ta Zargi Jami'an Mai









Kodayake matsalar mai ta fara lafawa a wasu sassan arewacin Najeriya, ganin yadda matsalar ta dada rikita al’amura a arewa maso gabashin Najeriya, musamman ma jahar Barno, Kungiyar ‘Yan Jarida (NUJ), shiyyar jahar ta daga yatsa ma manyan ma’aikatan bangaren man fetur, wadanda ta zarge da barin wasu masu zalama da haddasa matsalar.



Bayan yankin arewa maso gabashin Najeriya ya sha fama da karancin da kuma tsadar mai, musamman ma wanda aka yi kwanan nan, Kungiyar ‘Yan Jaridar Najeriya Shiyyar jahar ta Barno ta zargi manyan ma’aikatan bangaren main a Najeriya da rashin tabukawa sosai wajen dakile matsalar.

Kungiyar ta yi nuni da yadda Mataimakin Shugaban Najeriya Furfesa Yomi Osunbajo ya yi ta kai koma wajen ganin matsalar ta kau. Kungiyar ta ce sam manyan ma’aikatan bangaren mai bas u taimakawa kuma sun bar wasu manyan ‘yan kasuwa na cin karensu ba babbaka.

Da yake karin haske ma wakilinmu a jahar Barno, Haruna Dauda, Shugaban kungiyar ‘yan jaridar, Shiyyar jahar Barno, Baba Sheikh Haruna y ace ya zama wajibi su fitar da takardar yin Allah wadai da manyan jami’an bangaren mai din saboda yadda su ka bari masu son kazamin ribi na ta gasa ma jama’a aya a hannu. Ga Haruna Dauda da cikakken rahoton:

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

KUNGIYAR MURYAR TALAKA TA BAYAR DA TALLAFIN KAYAN MAKARANTA, GA DALIBBAI DA KADDAMAR DA SHUWAGABANNINTA A KARAMAR HUKUMAR MARU!

A yau Talata 19-12-2017 kungiyar Muryar Talaka ta kasa Reshen Jahar Zamfara. Kai ziyara a Karamar hukumar Maru domin bayar da tallafin kayan karatu ga dalibbai a makarantun Gwamnati da ke wadannan karamar hukumar . A lokacin ziyarar wadda shugaban kungiyar na Jahar Zamfara, Comrade HAFIZU BALARABE GUSAU. ya jagoranta. Ya bayyana cewa, kungiyar Muryar Talaka ta bullo da wannan shirin ne, domin tallafawa, wajen cigaban bangaren ilimi a wannan jahar. Wanda hakan ne, ya sa kungiyar ta bullo da wannan shirin La'akkari da yadda wasu uwaye su ke da matukar rauni wajen daukar nauyin dawainiyar 'ya'yansu. Haka zalika hakan zai taimaka wajen habbaka sha'anin ILIMI a Jahar Zamfara. A lokacin da ya ke jawabi shugaban makarantar BANAGA SULE Primary school, Maru. Ya bayyana kungiyar muryar Talaka da cewa "Kungiya ce da ya kamata sauran kungiyoyi su yi koyi da ita. "Dan Haka ya kamata ku Kara jajircewa wajen aiki tukuru. Musamman ganin cewa kungiyar, ba kungiya ba ...