Skip to main content

Gwamnatin tarayya ta yi watsi da kudirin samar wa makiyaya filayen kiwo a jihohi



Gwamnatin tarayya ta ba kowace jiha damar daukan matakin da zai kawo karshen rikicin makiyaya a kasar

Gwamnatin tarayya ta yi watsi da kudirin samar wa makiyaya filayen kiwo a jihohi
Kwamitin mutane 10 da majalissar

zartarwa ta kafa dan kawo karshen hare-haren makiyaya wasu sassan kasar, ta ba kowace jiha damar daukan matakin da take ganin zai kawo karshen matsalar.

Kwamitin wanda mataimakin shugaban kasa, Ferfesa Yemi Osinbanjo yake jagoranta, ya hadda da gwamnonin jihar Zamfara, Kaduna, Adamawa, Benuwe, Filato, Ebonyi da Oyo.

Wani babban jami’in fadar shugaban kasa ya fadawa manema labaru a ranar Lahadi cewa, gwamnatin tarayya bata son ta tilasatawa jihohi yin abubuwan da basa son yi.

Gwamnatin tarayya ta yi watsi da kudirin samar wa makiyaya filayen kiwo a jihohi
Yace mataikamakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo, ya bayyana haka wani taro da suka yi.



Jami’in wanda baya son a bayyana sunan shi yace, mataimakin shugaban kasa ya lura da irin fargaban da wasu jihohi suka shiga akan kudirin gwamnatin tarrayya na ware makiyaya filayen kiwo.

Yace kwamitin ta yanke shawaran hada gwiwa da gwamnatin wajen karfafa hukumomin sharia da jami’an tsaro
Kwamitin ta na son a kara karafafa jami’an tsaro ta inda za su kama wandanda suke kashe-kashe da masu daukan nauyin su a fadin kasar.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020