Skip to main content

YA KAMATA JAM'IYYUN ADAWA A JIHAR ZAMFARA SU ƘAURACEWA BABBAN ZAƁEN GWAMNONI DA NA 'YAN MAJALISUN JIHA DAKE TAFE




Ko shakka babu; kamar yadda ta bayyana ƙarara a zaɓen da ya gudana na shugaban Ƙasa da na 'yan Majalisun tarayya a ranar 23 ga fabrairun makon da ya gabata, irin yadda anka samu tarin matsaloli wajen yin zaɓen, Jam'iyyar APC mai ƙarfin fada a ji a cikin jihar ta Zamfara ita tayi uwa, tayi makarɓiya a cikin zaɓen, ma'ana dai ina nufin jam'iyyar tayi amfani da karfin ikon da take da shi, wajen cin karanta ba babbaka a dukkanin inda aka gabatar da zaɓen duk da kasancewar ita shugabar zaɓe ta jihar Zamfara ta tabbatar da za'ayi zaɓe mai cike da sahihanci da tsafta wanda kowa zaiyi na'am da shi.


A daidai lokacin da aka wayi garin safiyar zuwa runfunan zaɓe wato ranar Asabar, an samu wasu matsaloli, ta fuskar jinkirin kai kayan zaɓe da wuri, inda wasu rahotannin da muka samu daga wasu jihohin ƙasar nan daban-daban sun dade da fara jefa kuri'unsu, alhali kuma a nan jihar Zamfara ba'a kai kayan zabe ba, duk da tabbacin da hukumar shirya zabe ta ƙasa ta bayar na kammala kai kayan zaben a dukkanin lunguna da sakunan jihar ta Zamfara.


Babbar jam'iyyar APCn a jihar Zamfara ta sauyawa talakawan jihar Zamfara  tunane; irin yadda tayi amfani da maƙuddan kudaden Baitil malin gwamnati, wajen siyen masu kada kuri'a ta hanyar baiwa masu kaɗa kuri'a kudi domin zaben jam'iyyar Apc, kasancewar jam'iyyun Adawa a jihar ta Zamfara basu da isasun kuɗaɗen da zasu baiwa al'umma domin jefa musu ƙuri'u.

Duk da Hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yiwa tattalin arzikin ƙasa Tu'annati wato EFCC, Ta gargaɗi 'yan siyasa da bada kudade a lokacin da ake gabatar da zaɓuɓɓaka, amma hakan baiyi tasiri ba, damin masu ƙudi sunyi amfani da kudade wajen sayen masu kaɗa kuri'a a lunguna da saƙunan jihar Zamfara.


Kasancewar gwamnati ta tara komai, haƙiƙa za tayi amfani da wannan damar wajen yin abinda taga dama. Kamar yadda ya faru a zaben da ya gudana, 'ko shakka babu hakan zai faru a zaɓe mai zuwa', abisa wannan nake ganin kamar zaifi dacewa jam'iyyun Adawa su ƙauracewa zaben, saboda yana tattare da rashin adalci da aringizo!


Muna Addu'a da fatan Alheri. Ya Allah ka kawoma jihar Zamfara zaman lafiya da aminci da kwanciyar hankali da wadata.

Allah ya taimaki jihar Zamfara da al'ummarta da masu yi mata fatan Alheri baki daya.

Nagode


Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...