Skip to main content

Zuwa Ga Mai Daraja Gwamnan Jihar Zamfara a Kan Makomar Jihar



Zamfara jihace wadda a cikin kasar nan idon akayi magana a kan zaman lafiya ita ce kan gaba kafin wasu jihohi, shekaru 20 da suka gaba ta, duk wani dan jihar Zamfara idon zai kwanta bacci baya rufe gidansa. Mafi yawa daga cikin gidajen al'umma a wancen lokaci bud'e suke kwana har safe, saboda zaman lafiya. A wancen lokacin komai dare mutum baya jin tsoron tashi daga wannan gari zuwa wancen, daga wannan unguwa zuwa waccen, domin baya tsaron komai. 

A wancen lokacin dabbobi suna kwana a cikin daji, alhali mai su yana cikin gari hankalinsa akwance a natse! Baya tsoro wani abu. 

Dukkan kasuwannin dake fadin jihar suna gudana cikin dadin rai, duk da ana kallon a wancen lokacin kamar arziki bai yilwatu ba a cikin al'umma, amma zaman lafiya ya samu, kwanciyar hankali a ko'ina. Al'umma suna gudanar da rayuwarsu irin yadda suke so, babu tsamgwama, babu hantara, ko kyara!

Kaiconmu!

Duk wanda ya rayu a wancen lokacin, kuma yana raye a yanzu, ya ga abin mamaki da fargaba. Ganin irin yadda komai ya tab'arb'are dole ya zubar da hawaye, domin ko a cikin bacci dan Zamfara bai tab'a yin mafarkin zai samu kansa a cikin wannan yanayi ba. 

Sanadiyar matsalar tsaro dake damunmu a jihar Zamfara, komai ya lalace. Kasancewar babu yadda za'ayi a samu arziki da salama babu zaman lafiya. Zaman lafiya shine kashin bayan ci gaba kowace al'umma a rayuwa. 

Yanzu kauyuka da birane babu yadda a tsakaninsu, al'ummomi babu yadda. Ba a ga-maciji tsakanin manoma da Fulani makiyaya. Akwai tada hankali idan ana lissafa dubban mutanen da sunka rasa rayukansu hadi da cilastawa dubban wasu jama'ar barin muhallansu, kuma milyoyin nairori da anka tafka asara sakamakon wannan mumman tashin hankali basu lissafuwa.

Babu shakka lokaci yayi da ya kamata a cire siyasa, a tashi tsaye kai da fata, wajen samar da zaman lafiya a tsakanin al'umma. 

Babban burin talaka duk baifi a samar masa da zaman lafiya ba, a baiwa 'ya'yansa ilimi, a samar masa da ruwan sha, da hanyoyi da kuma kula da lafiyarsa, amma wannan ya gagara. Kaicon talaka a yau! 

Idon gari babu al'umma, ta yaya za'a samu jagora? Idon gari babu jama'a ta yaya za'a samu jin dadin shugabanci? Idon babu zaman lafiya ta yaya za a samu arziki ? Duk lokacin da al'umma sun ka kasance cikin fargaba da tashin hankali, to babu yadda za'ayi komai ya daidaita.

A bisa wannan nake kira ga shugabannimu a mataki daban-daban da cewa ya kamata suji tsoron Allah, kuma su san komai dadewa inda rayuwar talaka ta tafi, suma komai dadewa dole su bakunci wajen, kuma Allah ya nan madakata. Ya kamata su dawo cikin haiyacinsu, su hada kansu, su tsaya da murya daya, a matsayin tsintsinya madauri daya domin su kawo mana karshe wannan tashin hankali.

Wallahi wallahi al'umma suna cikin tashin hankali da fargaba, musamman mazauna kauyuka, wallahi basu iya bacci idon dare yayi , wasun su a daji suke bacci saman bishiyoyi. 

Muna kira da babbar murya da a daina sanya siyasa a cikin harkar tsaro, domin sanya siyasa a ciki baya kaiwa ga nasara. Al'ummarmu suna bukatar agaji. A taimaka don Girman Allah!

Ya ubangiji muna rokonka da sunayenka masu tsarki, da suffofinka madaukaka, ya Allah ka kawo mana zaman lafiya da aminci a jiharmu ta Zamfara, Arewa da Najeriya baki daya. Ya Allah ba don halinmu ba. Ka zama gatanmu.

Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.