Skip to main content

Zuwa Ga Mai Daraja Gwamnan Jihar Zamfara a Kan Makomar Jihar



Zamfara jihace wadda a cikin kasar nan idon akayi magana a kan zaman lafiya ita ce kan gaba kafin wasu jihohi, shekaru 20 da suka gaba ta, duk wani dan jihar Zamfara idon zai kwanta bacci baya rufe gidansa. Mafi yawa daga cikin gidajen al'umma a wancen lokaci bud'e suke kwana har safe, saboda zaman lafiya. A wancen lokacin komai dare mutum baya jin tsoron tashi daga wannan gari zuwa wancen, daga wannan unguwa zuwa waccen, domin baya tsaron komai. 

A wancen lokacin dabbobi suna kwana a cikin daji, alhali mai su yana cikin gari hankalinsa akwance a natse! Baya tsoro wani abu. 

Dukkan kasuwannin dake fadin jihar suna gudana cikin dadin rai, duk da ana kallon a wancen lokacin kamar arziki bai yilwatu ba a cikin al'umma, amma zaman lafiya ya samu, kwanciyar hankali a ko'ina. Al'umma suna gudanar da rayuwarsu irin yadda suke so, babu tsamgwama, babu hantara, ko kyara!

Kaiconmu!

Duk wanda ya rayu a wancen lokacin, kuma yana raye a yanzu, ya ga abin mamaki da fargaba. Ganin irin yadda komai ya tab'arb'are dole ya zubar da hawaye, domin ko a cikin bacci dan Zamfara bai tab'a yin mafarkin zai samu kansa a cikin wannan yanayi ba. 

Sanadiyar matsalar tsaro dake damunmu a jihar Zamfara, komai ya lalace. Kasancewar babu yadda za'ayi a samu arziki da salama babu zaman lafiya. Zaman lafiya shine kashin bayan ci gaba kowace al'umma a rayuwa. 

Yanzu kauyuka da birane babu yadda a tsakaninsu, al'ummomi babu yadda. Ba a ga-maciji tsakanin manoma da Fulani makiyaya. Akwai tada hankali idan ana lissafa dubban mutanen da sunka rasa rayukansu hadi da cilastawa dubban wasu jama'ar barin muhallansu, kuma milyoyin nairori da anka tafka asara sakamakon wannan mumman tashin hankali basu lissafuwa.

Babu shakka lokaci yayi da ya kamata a cire siyasa, a tashi tsaye kai da fata, wajen samar da zaman lafiya a tsakanin al'umma. 

Babban burin talaka duk baifi a samar masa da zaman lafiya ba, a baiwa 'ya'yansa ilimi, a samar masa da ruwan sha, da hanyoyi da kuma kula da lafiyarsa, amma wannan ya gagara. Kaicon talaka a yau! 

Idon gari babu al'umma, ta yaya za'a samu jagora? Idon gari babu jama'a ta yaya za'a samu jin dadin shugabanci? Idon babu zaman lafiya ta yaya za a samu arziki ? Duk lokacin da al'umma sun ka kasance cikin fargaba da tashin hankali, to babu yadda za'ayi komai ya daidaita.

A bisa wannan nake kira ga shugabannimu a mataki daban-daban da cewa ya kamata suji tsoron Allah, kuma su san komai dadewa inda rayuwar talaka ta tafi, suma komai dadewa dole su bakunci wajen, kuma Allah ya nan madakata. Ya kamata su dawo cikin haiyacinsu, su hada kansu, su tsaya da murya daya, a matsayin tsintsinya madauri daya domin su kawo mana karshe wannan tashin hankali.

Wallahi wallahi al'umma suna cikin tashin hankali da fargaba, musamman mazauna kauyuka, wallahi basu iya bacci idon dare yayi , wasun su a daji suke bacci saman bishiyoyi. 

Muna kira da babbar murya da a daina sanya siyasa a cikin harkar tsaro, domin sanya siyasa a ciki baya kaiwa ga nasara. Al'ummarmu suna bukatar agaji. A taimaka don Girman Allah!

Ya ubangiji muna rokonka da sunayenka masu tsarki, da suffofinka madaukaka, ya Allah ka kawo mana zaman lafiya da aminci a jiharmu ta Zamfara, Arewa da Najeriya baki daya. Ya Allah ba don halinmu ba. Ka zama gatanmu.

Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...