Skip to main content

KYAUTAR GIRMAMAWA DAGA YAZEED TRUST FUND ZUWA GA JEKADIYYAR YAZEED



Shimfiɗa.


Lambar yabo ta girmamawa wanda ake kira da (award) a turance wata babbar kyauta ce wadda ake bayarwa ga dukkan wanda ya shahara ta wasu fuskoki, misali; wanda ya kasance ɗan gwagwarmayar rayuwa a gefen da ya fi shahara haɗi da kwarewa, domin ƙara masa kwarin gwiwar tashi tsaye domin kara azama akan abinda yasa a gaba, domin ganin nasararsa ta ci gaba da ɗorewa har iyakar rayuwarsa. Madallah da lambar yabo ta girmamawa ga wanda ya cancanta!


A 19/08/2020 gidauniyar nan mai yaɗa manufofi haɗi da yin ayyukan alheri a cikin al'umma a duk faɗin jihar Zamfara, kuma mai son ganin al'umma sun samu kowane irin sauye-sauye ta fuskar  samarwa da jama'a ingantacciyyar rayuwa, wadda ke ƙarƙashin kulawar (Alh Yazeed Shehu Dan Fulani) wanda (Comrade Rufa'i Bala UB Gusau) yake shugabanta wato; (Yazeed Trust Fund) ta karrama daya daga cikin jiga-jigan gidauniyar, wato; (Hajiya Aisheet Ibraheem, mai laƙabi da 'yar Asali'.


An dubi yiwuwar, haɗi da nazarin bata wannan kyautar ne la'akari da irin ƙoƙarin da ta ke bayarwa wajan ci gaban tafiyar (Alh Yazeed Shehu Dan Fulani Mai Doya Garkuwan Matasan Gusau, Lamiɗon Tsafe). An yi hakan ne domin ƙara mata karsashi haɗi da kwarin gwiwar tsayuwar tsayin daka wajan fafutikar ci gaban al'umma ta kowane fanni. 



Dukkan masu ruwa da tsaki a cikin tafiyar gidauniyar Yazeed Trust Fund ne suka aminta da wannan kuduri, haka a lokacin da bikin bayar da wannan kyautar ke gudana, an kara karrama ta da kyautar Jakadiyar Yazeed, la'akari da cancantarta na rike wannan kambu, muna fatan hakan zai zama silar kara tsayuwa a cikin wannan tafiya.


Wasu daga cikin kungiyoyin fafutika da dama sun samu damar halartar wannan taro, da muhimman mutane da dama, a lunguna da sakunan jihar Zamfara da wasu daga cikin maƙotan jihar Zamfarar. Da dukkan takwarorinta mata da suka halarci wajan domin taya murna haɗi da shedar da bada wannan kyautar.


Jekadiyyar Yazeed ɗin a nata jawabi ta bayyana farin cikinta marar bisaltuwa haɗi da rera wasu baituka na yabo ga fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad (S.A.W), kasancewarta fasihiyar mawaƙiya wadda ke isar da saƙonni cikin hikima.


'yar Asalin, kuma. Tayi addu'ar Allah ya maida kowa gida lafiya, haɗi da addu'ar Allah ya bar zumunci. Kuma ya kara basu hakurin haɗin kai domin aiki tare wajan ciyar da jiha dama ƙasa baki daya a gaba.


Taron wanda ya gudana a Nafes (NFirst Hotel) a kan titin shiyar Samaru a tudun wada Ƙaramar Hukumar Gusau a jihar Zamfara, ya gudana kuma ya kammala lafiya.


Allah ya taimaki Jakadiyyar Yazeed.


Allah ya taimaki Alh Yazeed Shehu Danfulani


Allah ya taimaki Yazeed Trust Fund


Allah ya taimaki shugabanni da membobin Yazeed Trust Fund


Allah ya taimaki Gusau da Jihar

  Zamfara da Najeriya baki daya..



Rahoto


(Mai Apple).


Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...