Skip to main content

KYAUTAR GIRMAMAWA DAGA YAZEED TRUST FUND ZUWA GA JEKADIYYAR YAZEED



Shimfiɗa.


Lambar yabo ta girmamawa wanda ake kira da (award) a turance wata babbar kyauta ce wadda ake bayarwa ga dukkan wanda ya shahara ta wasu fuskoki, misali; wanda ya kasance ɗan gwagwarmayar rayuwa a gefen da ya fi shahara haɗi da kwarewa, domin ƙara masa kwarin gwiwar tashi tsaye domin kara azama akan abinda yasa a gaba, domin ganin nasararsa ta ci gaba da ɗorewa har iyakar rayuwarsa. Madallah da lambar yabo ta girmamawa ga wanda ya cancanta!


A 19/08/2020 gidauniyar nan mai yaɗa manufofi haɗi da yin ayyukan alheri a cikin al'umma a duk faɗin jihar Zamfara, kuma mai son ganin al'umma sun samu kowane irin sauye-sauye ta fuskar  samarwa da jama'a ingantacciyyar rayuwa, wadda ke ƙarƙashin kulawar (Alh Yazeed Shehu Dan Fulani) wanda (Comrade Rufa'i Bala UB Gusau) yake shugabanta wato; (Yazeed Trust Fund) ta karrama daya daga cikin jiga-jigan gidauniyar, wato; (Hajiya Aisheet Ibraheem, mai laƙabi da 'yar Asali'.


An dubi yiwuwar, haɗi da nazarin bata wannan kyautar ne la'akari da irin ƙoƙarin da ta ke bayarwa wajan ci gaban tafiyar (Alh Yazeed Shehu Dan Fulani Mai Doya Garkuwan Matasan Gusau, Lamiɗon Tsafe). An yi hakan ne domin ƙara mata karsashi haɗi da kwarin gwiwar tsayuwar tsayin daka wajan fafutikar ci gaban al'umma ta kowane fanni. 



Dukkan masu ruwa da tsaki a cikin tafiyar gidauniyar Yazeed Trust Fund ne suka aminta da wannan kuduri, haka a lokacin da bikin bayar da wannan kyautar ke gudana, an kara karrama ta da kyautar Jakadiyar Yazeed, la'akari da cancantarta na rike wannan kambu, muna fatan hakan zai zama silar kara tsayuwa a cikin wannan tafiya.


Wasu daga cikin kungiyoyin fafutika da dama sun samu damar halartar wannan taro, da muhimman mutane da dama, a lunguna da sakunan jihar Zamfara da wasu daga cikin maƙotan jihar Zamfarar. Da dukkan takwarorinta mata da suka halarci wajan domin taya murna haɗi da shedar da bada wannan kyautar.


Jekadiyyar Yazeed ɗin a nata jawabi ta bayyana farin cikinta marar bisaltuwa haɗi da rera wasu baituka na yabo ga fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad (S.A.W), kasancewarta fasihiyar mawaƙiya wadda ke isar da saƙonni cikin hikima.


'yar Asalin, kuma. Tayi addu'ar Allah ya maida kowa gida lafiya, haɗi da addu'ar Allah ya bar zumunci. Kuma ya kara basu hakurin haɗin kai domin aiki tare wajan ciyar da jiha dama ƙasa baki daya a gaba.


Taron wanda ya gudana a Nafes (NFirst Hotel) a kan titin shiyar Samaru a tudun wada Ƙaramar Hukumar Gusau a jihar Zamfara, ya gudana kuma ya kammala lafiya.


Allah ya taimaki Jakadiyyar Yazeed.


Allah ya taimaki Alh Yazeed Shehu Danfulani


Allah ya taimaki Yazeed Trust Fund


Allah ya taimaki shugabanni da membobin Yazeed Trust Fund


Allah ya taimaki Gusau da Jihar

  Zamfara da Najeriya baki daya..



Rahoto


(Mai Apple).


Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020