Skip to main content

Sabunta Riyoji a Cikin Gusau!



A yau ne Assabar 18/07/2020 Gidauniyar Yazeed Trust Fund ta gudanar da gyaran wasu riyojin fanfuna a filin na yawo dake shiyar Sabon fege a Cikin gundumar Galadima a karamar Hukumar Gusau ta jihar Zamfara. Gyaran na zuwa ne a daidai lokacin da al'umma ke matukar neman bukatar taimako musamman abunda ya shafi bangaren samar da ruwan sha masu tsafta.


A ci gaba da rangadin bayar da kowane irin taimako hadi da bada gudunmuwa a cikin al'umma, tawagar Gidauniyar Yazeed tayi kicibus da wasu riyoji da ake ci gaba da ibar ruwa a ciki, duk da kasancewar akwai kwatoci da sauran wasu ledodi da kayan kazanta.

Kai tsaye jakadun Alh Yazeed Shehu Danfulani karkashin jagorancinsa, ta hannun shugaban amintattun gudanarwa na tafiyar, kuma shugaban kungiyar Yazeed Trust Fund Comrade Rufa'i Bala UB Gusau, suka dukufa ka'in da Na'in wajan gyaran riyojin, domin sabuntasu hadi da mayar da su sabbi, ta hanyar saka masu Tayis da kuma yi masu aiki na zamani, domin samar da ruwa masu tsafta a cikin al'umma.

Babban wani abun sha'awa shine irin yadda al'ummar wannan yanki sun ka nuna farin cikinsu marar misaltuwa a lokacin gudanar da aikin, gungun matasa hadi da dattawa, da matan wannan yanki sun nuna matukar farin cikinsu, hadi da sambarka. Tare da addu'a da fatan alheri.

Wani abun sha'awa shine, wani fitaccen malamin addinin islama dake a yankin mai suna; Malam Dan Hajo, wanda kuma shine wanda yayi addu'ar bude wadannan rojiyoyi yace ko shakka babu, shi yafi kowa sanin halin Alh Yazeed Domin kuwa a makarantarsa yayi karatu shi da ahalinsa, sannan ya samu kyakkyawar tarbiyya shiyasa ba yayin kasa a gwiwa wajan gudanar da ayyukan alheri a cikin al'umma. Sannan ya kara da jan hankali akan fadada wannan hidima a nan gaba, wajan yin irin wadannan gyare-gyare a makarantun allo wadanda ke matukar bukatar hakan.

A lokacin da muka tuntubi daya daga cikin jiga-jigan tafiyar Alh Yazeed Shehu Danfulani, kuma jigo a Gidauniyar Yazeed Trust Fund, Kaura Na Madina, ya tabbar da cewar wannan ba shine karo na farko ba, na gudanar da aikin sabunta riyoji a cikin Gusau babban birnin jihar Zamfara.

A lokacin da muka mayar da abin magana ga shugaban tafiyar, wato COMRADE UB GUSAU, ya ce ya kara da jaddada mana cewar ko shakka babu ire-iren wadannan ayyukan ba zasu kyargu ba, sannan za'a cigaba da gudanar da su a cikin al'umma, ba tare da nuna bambanci ba.

Idan dai masu karatu zasu iya tunawa, ko in ba su manta ba, mun sha kawo maku wasu kadan daga cikin ayyukan alherin da Alh Yazeed Shehu Danfulani yake a cikin al'umma. Domin ganin ya bayar da duk wata gudunmuwar da ake bukata iya karfinsa.


Kama tun daga makarantu, daukar nauyin karatu, samar da ruwan sha. Kiyon lafiya. Da sauransu.

A karshe muna addu'ar Allah ya ci gaba da taimakon Alh Yazeed Shehu Danfulani, Garkuwan Matasan Gusau Lamidon Tsafe, a kan manufofinsu na alheri a cikin al'umma.

Fatan Alheri Gusau
Fatan Alheri Zamfara
Fatan Alheri Najeriya
fatan Alheri Afrika



Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...