Skip to main content

Matasan Ɗan Bedi sun nemi haɗin gwiwa wajan ayyukan alheri da Yazeed Trust Fund

YAZEED TRUST FUND MEDIA


  A cikin kowane lokaci wannan tafiyar tana kara samun tagomashi, inda cikin ikon Allah wasu zaratan matasa da dattawa suka yi haɗin  gwiwa ga tafiyar matashin dattijo (Alh Yazeed Shehu Ɗanfulani garkuwan matasan Gusau Lamidon Tsafe)  ko shakka babu a cikin kowace tafiya ana son samun mutum kamilalle irin Alh Yazeed, kasancewarsa mutum mai son ganin mutane cikin walwala da kwanciyar hankali, domin sai al'umma suna cikin walwala ne sannan zasu samu damar gudanar da lamurran yau da kullum.



Idan mukayi la'akari da a kowane lokacin faɗi tashinsa shine bayar da tallafi ga masu ɗan ƙaramin karfi, a Bisa duba da irin ayukkan alherin da yake yi don ganin ya kawo ma Al'umma sauyin rayuwa, wannan ne yasa wadannan matasa sun ka ga dacewar tuntuɓa domin ganin su kansu sun bayar da kowace irin gudunmuwa a cikin wannan tafiya, ta Alh Yazeed Shehu Ɗanfulani. 


Matasan haɗi da dattawan,  sunyi alkawarin zasuyi wannan tafiya ba tare da jin wani ɗar a zuciyarsu ba, domin suma sun haƙiƙance cewa zasu iya bada tasu gudunmuwa a cikin Al'umma don suyi koyi da wannan matashi Mai rikon amana.

A lokacin gabatar da nasa jawabin ga al'ummar yankin, shugaba mai kula da wannan gwagwarmayar samun cigaba (Comrd Rufa'i Bala UB Gusau) ya godewa Allah, kuma ya godewa al'ummar wannan yanki a bisa yin dogon nazari da hangen nesa da suka yi wajan ganin sun shigo an hadu waje daya don ciyar da al'umma dama jiha baki daya a gaba, a karshe yayi addu'ar Allah ya cigaba da zama gatan mai taimakon Al'umma a duk indan yake.

Da fatan Allah ya cigaba da daukaka garkuwan matasa ya kuma biya masa dukkan bukatunsa na alheri Don alfarmar manzon Allah ( S,A,W )

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.