Skip to main content

SAKAMAKON ZABEN JIN RA'AYIN JAMA'A NA MURYAR TALAKA YA NUNA KANSILAN GUNDUMAR GALADIMA, GUSAU (HON. UMAR KWACCIDO) NE GWARZON KANSILA, NA ZAMFARA!

SAKAMAKON ZABEN JIN RA'AYIN JAMA'A NA MURYAR TALAKA YA NUNA KANSILAN GUNDUMAR GALADIMA, GUSAU (HON. UMAR KWACCIDO) NE GWARZON KANSILA, NA ZAMFARA!



Kamar yadda Kungiyar MURYAR TALAKA RESHEN JAHAR ZAMFARA ta shirya zaben jin ra'ayin jama'a akan Wanda ya dace ya zama GWARZON KANSILA a tsakanin takwarorinsa na Jahar Zamfara.

Hon. Umar Kwacchido, Gusau. Bayan ya zama zababben KANSILA a mazabar Galadima dake Gusau, an shede shi da kyakkyawan hali da riko da addinin isalama da ma son talakkawan da ya ke cikinsu.

Domin karrama shi tare da kara masa karfin guiwar cigaba da yiwa al'ummarsa ayukkan azo a gani. Wanda Hakan zai kara karfafa takwarorinsa, wajen kula da Al'umma.

la'akkari da wadannan hujjoji kamar haka da al'umma sunka fada akan wannan KANSILA;

1- BANGAREN YAKI DA FATARA.

* Ya sayawa matasa Babura suna kabu-kabu har 42 a yankin Galadima, inda mutun za su biya shi, kudin duk sati Dubu biyar har su mallake shi.

* Haka zalika ya baiwa 'yan Kasuwa talatin (30) kowane Dubu hamsin-hamsin bashi a yankinsa, duk Wata su biya Dubu biyar.

BANGAREN ADDINI

* Ya gina masallaci a shiyar tudun faila.
Tare da bayar da gudummuwa zuwa ga masallatan hamsussulawat. Da tabarmi da sauransu.

* Ya Shirya Musabakar al'kur'ani a matakin yankinsa na Galadima

BANGAREN NEMAN ILIMI

* Ya dunka kaya da sanya yara makarantar Firamare  har mutun 600.

*Ya dunka kaya da sanya yara makarantar Sikandare su  har mutun 200

* Yakan taimakawa ya yan Makaranta domin zana Jarabawar kammala Sikandare.

* Ya kai matasa 15 a  makarantun gaba da Sikandare 5 a zacas 5  maru 5 Tsafe

* Shirya musabaka ta yan makarantun islamiya dake mazabarsa.

*Ya Gina Toilet a makarantar primary ta Malam wakkala dake hayin Mlm Ibrahim mai Tafseer.

*Yana kokarin samawa Matasan da ke kokarin wuce makarantar gaba da Sikandare takardar shedar zama 'yan yanki (indigent)

*Yana sayawa matasa masu kokarin shiga aikin kaki form a duk lokacin da Hakan ta tusgo.

BANGAREN AYUKKA DA YA YINA MUSAMMAN.

*  Taimakawa wajen gyara wata gada dake daura da nasiha kyamis dake mazabarsa, duk dacewa aikin na karamar hukuma ne. kwalbatin shiga kurmi da ta lalace, kwalbatin Dan durumi, Daura da Gidan Alh. Tukur Muhammad, kofar Jange, gyaran kwalbati a kofar Gidan Mamanu Sabon Fege

* Ya raba  Babura companion 6 a yankisa.

* Ya bada tallafi ga wanda bala'in ruwan sama ya sama a damanar bana na cement 200 da bulo 1000.

ya gina fanfonda ke bada ruwa fiyeda shekara bakwai har yanzu ana anfana dashi (wato kusada gidan marigayi Bala na Mada sabon fegi).

la'akkari da wadannan kwakkwaran dalillai da kyakkyawan ayukkan, Kungiyar MURYAR TALAKA ta yi Dogaro. Har ta aminta da cewa shi ne ya fi dukkannin takwarorinsa Kansiloli a Jahar Zamfara, Dan Haka zata baiwa wannan Dan tahalikin Lambar YABO a Babban taron Kungiyar da za ta yi a watan 3-2018 a Matsayin Kwarzon KANSILA a Jahar Zamfara.

Muna Taya shi murna, Allah ya ba shi ikon cigaba da yiwa Al'ummarsa abubuwan kirki, muna rokon Allah ya sa wannan kyautar ta kara masa azama. Daga karshe muna rokon Allah ya ba shi Wata kujera da ta fi wannan a 2019 domin cigaba da yiwa Al'umma hidima.

Abdulmalik Saidu Mai Biredi Tashar Bagu Gusau PRO I MURYAR TALAKA RESHEN JAHAR ZAMFARA. Da Nura Muhammad Mai Apple Gusau,  A madadin dukkanin shuwagabannin Kungiyar da membobinmu.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

KUNGIYAR MURYAR TALAKA TA BAYAR DA TALLAFIN KAYAN MAKARANTA, GA DALIBBAI DA KADDAMAR DA SHUWAGABANNINTA A KARAMAR HUKUMAR MARU!

A yau Talata 19-12-2017 kungiyar Muryar Talaka ta kasa Reshen Jahar Zamfara. Kai ziyara a Karamar hukumar Maru domin bayar da tallafin kayan karatu ga dalibbai a makarantun Gwamnati da ke wadannan karamar hukumar . A lokacin ziyarar wadda shugaban kungiyar na Jahar Zamfara, Comrade HAFIZU BALARABE GUSAU. ya jagoranta. Ya bayyana cewa, kungiyar Muryar Talaka ta bullo da wannan shirin ne, domin tallafawa, wajen cigaban bangaren ilimi a wannan jahar. Wanda hakan ne, ya sa kungiyar ta bullo da wannan shirin La'akkari da yadda wasu uwaye su ke da matukar rauni wajen daukar nauyin dawainiyar 'ya'yansu. Haka zalika hakan zai taimaka wajen habbaka sha'anin ILIMI a Jahar Zamfara. A lokacin da ya ke jawabi shugaban makarantar BANAGA SULE Primary school, Maru. Ya bayyana kungiyar muryar Talaka da cewa "Kungiya ce da ya kamata sauran kungiyoyi su yi koyi da ita. "Dan Haka ya kamata ku Kara jajircewa wajen aiki tukuru. Musamman ganin cewa kungiyar, ba kungiya ba ...