Skip to main content

SAKAMAKON ZABEN JIN RA'AYIN JAMA'A NA MURYAR TALAKA YA NUNA KANSILAN GUNDUMAR GALADIMA, GUSAU (HON. UMAR KWACCIDO) NE GWARZON KANSILA, NA ZAMFARA!

SAKAMAKON ZABEN JIN RA'AYIN JAMA'A NA MURYAR TALAKA YA NUNA KANSILAN GUNDUMAR GALADIMA, GUSAU (HON. UMAR KWACCIDO) NE GWARZON KANSILA, NA ZAMFARA!



Kamar yadda Kungiyar MURYAR TALAKA RESHEN JAHAR ZAMFARA ta shirya zaben jin ra'ayin jama'a akan Wanda ya dace ya zama GWARZON KANSILA a tsakanin takwarorinsa na Jahar Zamfara.

Hon. Umar Kwacchido, Gusau. Bayan ya zama zababben KANSILA a mazabar Galadima dake Gusau, an shede shi da kyakkyawan hali da riko da addinin isalama da ma son talakkawan da ya ke cikinsu.

Domin karrama shi tare da kara masa karfin guiwar cigaba da yiwa al'ummarsa ayukkan azo a gani. Wanda Hakan zai kara karfafa takwarorinsa, wajen kula da Al'umma.

la'akkari da wadannan hujjoji kamar haka da al'umma sunka fada akan wannan KANSILA;

1- BANGAREN YAKI DA FATARA.

* Ya sayawa matasa Babura suna kabu-kabu har 42 a yankin Galadima, inda mutun za su biya shi, kudin duk sati Dubu biyar har su mallake shi.

* Haka zalika ya baiwa 'yan Kasuwa talatin (30) kowane Dubu hamsin-hamsin bashi a yankinsa, duk Wata su biya Dubu biyar.

BANGAREN ADDINI

* Ya gina masallaci a shiyar tudun faila.
Tare da bayar da gudummuwa zuwa ga masallatan hamsussulawat. Da tabarmi da sauransu.

* Ya Shirya Musabakar al'kur'ani a matakin yankinsa na Galadima

BANGAREN NEMAN ILIMI

* Ya dunka kaya da sanya yara makarantar Firamare  har mutun 600.

*Ya dunka kaya da sanya yara makarantar Sikandare su  har mutun 200

* Yakan taimakawa ya yan Makaranta domin zana Jarabawar kammala Sikandare.

* Ya kai matasa 15 a  makarantun gaba da Sikandare 5 a zacas 5  maru 5 Tsafe

* Shirya musabaka ta yan makarantun islamiya dake mazabarsa.

*Ya Gina Toilet a makarantar primary ta Malam wakkala dake hayin Mlm Ibrahim mai Tafseer.

*Yana kokarin samawa Matasan da ke kokarin wuce makarantar gaba da Sikandare takardar shedar zama 'yan yanki (indigent)

*Yana sayawa matasa masu kokarin shiga aikin kaki form a duk lokacin da Hakan ta tusgo.

BANGAREN AYUKKA DA YA YINA MUSAMMAN.

*  Taimakawa wajen gyara wata gada dake daura da nasiha kyamis dake mazabarsa, duk dacewa aikin na karamar hukuma ne. kwalbatin shiga kurmi da ta lalace, kwalbatin Dan durumi, Daura da Gidan Alh. Tukur Muhammad, kofar Jange, gyaran kwalbati a kofar Gidan Mamanu Sabon Fege

* Ya raba  Babura companion 6 a yankisa.

* Ya bada tallafi ga wanda bala'in ruwan sama ya sama a damanar bana na cement 200 da bulo 1000.

ya gina fanfonda ke bada ruwa fiyeda shekara bakwai har yanzu ana anfana dashi (wato kusada gidan marigayi Bala na Mada sabon fegi).

la'akkari da wadannan kwakkwaran dalillai da kyakkyawan ayukkan, Kungiyar MURYAR TALAKA ta yi Dogaro. Har ta aminta da cewa shi ne ya fi dukkannin takwarorinsa Kansiloli a Jahar Zamfara, Dan Haka zata baiwa wannan Dan tahalikin Lambar YABO a Babban taron Kungiyar da za ta yi a watan 3-2018 a Matsayin Kwarzon KANSILA a Jahar Zamfara.

Muna Taya shi murna, Allah ya ba shi ikon cigaba da yiwa Al'ummarsa abubuwan kirki, muna rokon Allah ya sa wannan kyautar ta kara masa azama. Daga karshe muna rokon Allah ya ba shi Wata kujera da ta fi wannan a 2019 domin cigaba da yiwa Al'umma hidima.

Abdulmalik Saidu Mai Biredi Tashar Bagu Gusau PRO I MURYAR TALAKA RESHEN JAHAR ZAMFARA. Da Nura Muhammad Mai Apple Gusau,  A madadin dukkanin shuwagabannin Kungiyar da membobinmu.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.