Skip to main content

Uche Secondus Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar PDP



An zabi Uche Secondus a matsayin sabon shugaban babbar jam’iyyar adawa a Najeriya, PDP, bayan da aka kammala kidaya kuri’un zaben da aka gudanar jiya Asabar.

Tsohon mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP Prince Uche Secondus ne ya lashe zaben shugabancin jam’iyyar bayan kammala babban taron jam’iyyar da ya kawo karshen kwamitin riko na Sanata Ahmed Makarfi.

Secondus daga yankin kudu maso kudancin Najeriya, ya samu kuri’u 2000 inda ya yi nasara kan abokan takarar sa biyu Farfesa Tunde Adeniran da Chief Raymond Dokpesi.

Tun gabanin taron, wassu daga wadanda su ka aiyana tsayawa takarar da su ka hada da Bode George da Gbenga Daniel sun janye; inda har George ke zargin cewa gwamnan Rivers Nyesom Wike ya nunawa Yarbawa wariya musamman don mara baya ga Secondus.

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan, tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar daTom Ikimi da sauran gwamnonin jam’iyyar irin su Ayo Fayose da Ibrahim Dankwambo sun shaida sanarda sakamakon da a ka yi daidai karfe uku da minti goma sha biyar na safe agogon Najeriya.

Yanzu jam’iyyar za ta tura tikitin takarar shugaban kasa yankin arewa a shekarar 2019.

Alamu na nuna har yanzu gwamnoni na da tasirin juya lamurra a manyan jam’iyyun Najeriya.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...