Skip to main content

PDP Ta Zargi Gwamnatin Katsina Da Gaza Tabuka Abin Kirki

PDP Ta Zargi Gwamnatin Katsina Da Gaza Tabuka Abin Kirki







Jam`iyyar PDP mai adawa a Najeriya da kuma a Katsina ta yi zargin cewa tun lokacin da takwararta APC ta kwace mulkin jihar daga hannunta babu wani abin kirkin da ta tsinana wa jihar tsawon kimanin shekara uku.

Shugaban PDP a jihar Katsina, Alhaji Salisu Yusuf Majigiri ya ce ayyukan raya kasa sun tsaya cik, hatta wasu manyan ayyuka da gwamnatinsu ta fara aiwatarwa, amma ba ta kammala gabanin ta bar mulki ba, duk an yi watsi da su.

Ya ce ayyukan sun hadar da Kasuwar Dubai da kwalejin fasahar sadarwa, ya yi ikirarin cewa gwamnatin jihar ta fi mayar da hankali wajen runton aiki ta hanyar yi wa makarantun da gwamnatinsu ta gina fenti.

Haka zalika, PDP ta zargi jam’iyyar APC da karbo bashin biliyoyin naira ba tare da aiwatar da aikin a-zo-a-gani ba.

Sai dai APC ta musanta wadannan batutuwa, ta ce PDP ba ta da bakin magana idan aka yi la`akari da dumbin bashi da mawuyacin halin da ta bar al`ummar jihar a ciki.

Shi dai Majigiri na cewa: “Maganar ilmi da noma da kula da lafiya dukkansu ba bangaren da ya ci gaba, sai baya da muka mika mulki. Kuma mun bar kudi sun kai biliyan 14 a asusun gwamnati, sannan zuwa yanzu ta karbi sama da biliyan 300 amma a nuna min aikin wani aiki na miliyan 500 da za a iya budewa a jihar Katsina.”

Ya ce makarantun da gwamnatinsu ta bari ne, jam’iyyar APC take bi tana yi musu fenti maimakon fentin Najeriya da suke da shi. A cewarsa: Da ya ji ruwan damuna zai wanke, fenti aiki ne?”

Shugaban jam`iyyar APC na jihar Katsina, Alhaji Shitu Shuaibu Shitu ya ce hasali ma, kura-kura da PDP ta tafka ne suka jefa Katsina a halin da ta samu kanta, don haka bai kamata ta zake tana hakikicewa ba.

Ya ce zamanin mulkin PDP, gwamnatinsu ba ta dauki hakkin ma`aikata a bakin komai ba, duk kuwa da irin gudummuwar da suke bayarwa wajen raya kasa da ciyar da jihar gaba.

Jam`iyyar PDP ta shafe shekara 16 tana mulkin jihar Katsina. Sai a 2015 ne ta sha kaye a hannun jam`iyyar APC.

Manufar caccaka da sukar da abokan adawar siyasa kan yi dai, kamar yadda masana ke cewa, ita ce ankarar da jam`iyya mai mulki don ta gyara tafiyarta.

Amma a Najeriya ba kasafai jami`yya mai mulki ke kallon lamarin a matsayin gyara kayanka ba, sakamakon zargin cewa ba da kyakkyawar niyya aboakan hamayya kan yi hakan ba.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...