Skip to main content

PDP Ta Zargi Gwamnatin Katsina Da Gaza Tabuka Abin Kirki

PDP Ta Zargi Gwamnatin Katsina Da Gaza Tabuka Abin Kirki







Jam`iyyar PDP mai adawa a Najeriya da kuma a Katsina ta yi zargin cewa tun lokacin da takwararta APC ta kwace mulkin jihar daga hannunta babu wani abin kirkin da ta tsinana wa jihar tsawon kimanin shekara uku.

Shugaban PDP a jihar Katsina, Alhaji Salisu Yusuf Majigiri ya ce ayyukan raya kasa sun tsaya cik, hatta wasu manyan ayyuka da gwamnatinsu ta fara aiwatarwa, amma ba ta kammala gabanin ta bar mulki ba, duk an yi watsi da su.

Ya ce ayyukan sun hadar da Kasuwar Dubai da kwalejin fasahar sadarwa, ya yi ikirarin cewa gwamnatin jihar ta fi mayar da hankali wajen runton aiki ta hanyar yi wa makarantun da gwamnatinsu ta gina fenti.

Haka zalika, PDP ta zargi jam’iyyar APC da karbo bashin biliyoyin naira ba tare da aiwatar da aikin a-zo-a-gani ba.

Sai dai APC ta musanta wadannan batutuwa, ta ce PDP ba ta da bakin magana idan aka yi la`akari da dumbin bashi da mawuyacin halin da ta bar al`ummar jihar a ciki.

Shi dai Majigiri na cewa: “Maganar ilmi da noma da kula da lafiya dukkansu ba bangaren da ya ci gaba, sai baya da muka mika mulki. Kuma mun bar kudi sun kai biliyan 14 a asusun gwamnati, sannan zuwa yanzu ta karbi sama da biliyan 300 amma a nuna min aikin wani aiki na miliyan 500 da za a iya budewa a jihar Katsina.”

Ya ce makarantun da gwamnatinsu ta bari ne, jam’iyyar APC take bi tana yi musu fenti maimakon fentin Najeriya da suke da shi. A cewarsa: Da ya ji ruwan damuna zai wanke, fenti aiki ne?”

Shugaban jam`iyyar APC na jihar Katsina, Alhaji Shitu Shuaibu Shitu ya ce hasali ma, kura-kura da PDP ta tafka ne suka jefa Katsina a halin da ta samu kanta, don haka bai kamata ta zake tana hakikicewa ba.

Ya ce zamanin mulkin PDP, gwamnatinsu ba ta dauki hakkin ma`aikata a bakin komai ba, duk kuwa da irin gudummuwar da suke bayarwa wajen raya kasa da ciyar da jihar gaba.

Jam`iyyar PDP ta shafe shekara 16 tana mulkin jihar Katsina. Sai a 2015 ne ta sha kaye a hannun jam`iyyar APC.

Manufar caccaka da sukar da abokan adawar siyasa kan yi dai, kamar yadda masana ke cewa, ita ce ankarar da jam`iyya mai mulki don ta gyara tafiyarta.

Amma a Najeriya ba kasafai jami`yya mai mulki ke kallon lamarin a matsayin gyara kayanka ba, sakamakon zargin cewa ba da kyakkyawar niyya aboakan hamayya kan yi hakan ba.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.