Skip to main content

Fursunoni Mata Na Karuwa A Duniya

Fursunoni Mata Na Karuwa A Duniya




Wani bincike da aka gudanar a kan yawan mata da ‘yammatan da ke zaman gidan yari a sassan duniya daban-daban, ya gano cewa adadin matan ya karu musamman a shekarun baya-bayan nan.

Binciken ya kiyasta cewa yanzu haka akwai mata fiye da dubu dari bakwai da ke zaman gidan gidan kaso a duniya.

A cewar wata cibiyar da ke bincike kan manyan laifuka da ke birnin London, adadin matan da ke zaman gidan kaso na karuwa a kowacce nahiya a cikin shekaru 17 da suka wuce, kuma an fi samun karuwar adadin fursunoni mata ne a kasashen Brazil da Indonesia da Phillipines da kuma Turkiya.

Cibiyar ta ce, inda kuma ake da yawan fursunoni mata su ne Amurka da kuma China.

An daure matar da ce mata na iya haihuwa babu aure

‘Mata ba za su yi daidai da maza ba nan da shekara 100’

A shekarar 2015, China ta samu karuwar fursunoni mata da yawa wadanda suka aikata laifukan da suka hadar sa sarafar miyagun kwayoyi da kuma cin hanci inji cibiyar.

Hakan ya sa China ta zamo kasa ta biyu a duniya da ta ke da yawan fursunoni mata.

To amma duk da haka yawan fursunoni mata na China bai kai rabin fursunoni matan da ke Amurka ba.

Kuma wadannan fursunoni wasu na zaune ne kafin a yanke musu hukunci, yayinda wasu kuma ke zaman hukuncin da aka yanke musu.

Masu bincike sun ce ana kashe makudan kudade wajen kula da fursunoni mata, to amma duk da haka baya wani tasiri ko kadan idan sun dawo cikin al’umma.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...