Skip to main content

Dakarun Hadin Kan Afirka Zasu Fatattaki Mayakan Al-Shabab Daga Somalia

Dakarun Hadin Kan Afirka Zasu Fatattaki Mayakan Al-Shabab Daga Somalia






Dakarun hadin kan Afirka, AU, a Somalia

Dakarun kungiyar tarayyar Afirka ta AU sun kaddamar da wani shiri a kasar Somalia da zai fatattaki mayakan kungiyar al-Shabab daga yankin Shabelle, a kuma killace hanyar shigar da kayayyaki zuwa yankin.

Shaidu sun fadawa sashen Somaliyanci na Muryar Amurka cewa, sun ga sojojin kungiyar AU akan hanya da kuma wani yanki da ake noma tsakanin garin Afgoye da Bal’ad, sun kuma lura da cewa babu ‘yan kungiyar al-Shabab dayawa a yankin jiya Litinin.

Aikin da kungiyar tarayyar Afirka ke yi a Somaliya, da ake kira AMISOM, a wata sanarwa an fadi cewa an kaddamar da shi ne bayan da aka samu bayanai kan cewa kungiyar Al-Shabab na kawo rashin kwanciyar hankali a babbar hanyar da ta hada Mogadishu da filin saukar jiragen sama na Ballidogle, mai tazarar kilomita 90 arewa da babban birnin tarayya.

Ballidogle dai filin jiragen saman sojoji ne dake yankin Shabelle, inda dakarun Amurka ke horas da sojojin Somaliya.

Babu tabbacin ko harin da aka kai na jiya kan mayakan al-Shabab na wani bangare na zafafa hare-haren da sojojin Somali da na AU suke yi, amma shirin AMISOM yace shiri ne kan mayakan al-Shabab, kuma za a gudanar da shi sannu a hankali.

Shekaru biyu kenan tunda kungiyar AU ta kaddamar da hari kan kungiyar Al-Shabab.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020