Skip to main content

An Bukaci A Nisanta Addini Daga Bakar Akidar Boko Haram






Sakataren Kungiyar Kiristocin Najeriya Rabaran Musa Asake da Shugaban Kungiyar IZALA Shaikh Abdullahi Bala Lau a wurin kallon majigin da VOA ta shirya akan Boko Haram

Yayinda ake ci gaba da nuna majigin Muryar Amurka akan Boko Haram mai taken Tattaki daga Bakar Akida shugabannin addini sun bukaci a nisanta addini da akidar Boko Haran tare da kiran hadin kai tsakanin Kirista da Muslmi a Najeriya

A lokacinda ake nuna majigin Muryar Amurka kan yaki da bakar akidar Boko Haram malamai da kungiyoyin matasa sun nuna bukatar a bude sabon babi na nisanta addini daga muguwar masu kashe jama’a ba tare hakkin shari’a ba.

Shugaban kungiyar IZALA Abdullahi Bala Lau da sakataren kungiyar Kiristoci ta Najeriya Rabaran Musa Asake sun nuna takaicin yadda ‘Yan Boko Haram suka cuci al’ummar da basu da laifin komi.

Shaikh Abdullahi Bala Lau ya bukaci cewa a karantar da akida mai kyau. Yayi misali da irin gudummawar da Shaikh Jaafar Mahmud Adam ya bayar da har ya kai ga yi masa kisan gilla. Y ace duk wani malami kuma da yayi yunkurin yin wa’azi akan akidar Boko Haram sai a kasheshi. Dalili ke nan malamai da yawa sun tsorata basa iya fitowa fili su kalubalanci kungiyar Boko Haram ba.

Shi ma Rabaran Musa Asake ya nuna damuwa da yadda ya ce gwamnati tayi sakaci da yaki da Boko Haram tare da cewa majigin na VOA ya fadakar dashi akan bukatar dake akwai Kiristoci da Musulmai su hada kai wajen wanzar da zaman lafiya. Yace da shugabannin addinan biyu sun zauna akan matsalar Boko Haram da sun yi maganin kungiyar. A cewarsa yanzu idan mutum yayi magana sai a bishi ana neman a kasheshi.

Kungiyar matasan Najeriya karkashin shugabancin Murtala Garba da wasu sun halarci taron.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM GLOBAL INITIATIVES .... PRESS RELEASE ...

Good day Ladies and Gentlemen of the media.                       In the past few days, we were surprised to learn that few among our Foundation members posted online their official statement of resignation from Labour room cabinet. Despite mixed feelings, Let us start by stating the following: 1. We hereby acknowledge your  contributions to the dynamics of the Labour room. Though, letters were served to each and every appointment/portfolio. Its expected that you write to Labour room Leadership about your intentions rather than addressing it to the general public, but nonetheless, its all for good. 2. The leadership of the labour room global initiatives remain focused, as all those that resigned constitute less than 3% of the entire cabinet. 3. We remain committed to d service to humanity 4. Those outsiders that are not acquainted with the processes of the labour room and genesis of the matter should always endeav...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...