Skip to main content

Shiga Ta Harkar Fim Na Wucin Gadi Ne, Da Zarar Na Samu Miji Zan Yi Aure - Jarumar Hausa Fim Fati Garba.

Shiga Ta Harkar Fim Na Wucin Gadi Ne, Da Zarar Na Samu Miji Zan Yi Aure - Jarumar Hausa Fim Fati Garba.

Fati Garba shahararriyar yan wasan fina-finan Hausa ce da bata dade da shiga harakar ba. Sai dai shigar ta ke da wuya ta ko nuna hazakarta da kwazo wajen nuna cewa ita ma zata iya kara wa da manyan jarumai a farfajiyar fina-finan Hausa.

A hira da tayi da manema labarai a Abuja, ta ce Allah ne yayi za ta yi fim a Kannywood domin har ta cire rai.

” Na dade ina neman yadda zan yi in shiga farfajiyar Fina finan Kannywood amma inaa tunda har sai da na hakura ma domin duk ta inda na bi sai kaga ba haka ba. Abin ya gagara.”

Fati ta ce dama can tana dan yin wasannnin kwaikwayo a jihar Neja inda tun a wannan lokacin take ta kokarin samun daman shiga Kannywood.

” Cikin Ikon Allah kuwa wata rana wani da na sani ya ce zai sakani a wani fim da yake shiryawa kuma Jarumi Adam Zango ne zai fito a fim din. Nan da nan ko naji kamar ya yi mini Albishir da miliyoyin kudi. Dalili kuwa shine, Adama Zango na daga cikin wadanda nake son in ko da gansu ne mu gaisa a rayuwa ta sai gashi wai zan hadu da shine sannan kuma har kila in yi fim tare da shi.”

” Da yake fim din A Zariya a kayi sai ko gashi na hadu da Adamu Zango. Daga nan ya ce mu hadu a Kaduna inda ya ke shirya wani fin din sa. Aiko muna haduwa sai gashi ya saka ni a ciki kuma ma babban matsayi ya bani. Daga nan kuwa sai likkafata ta ci gaba.”

Fati ta kara da cewa ko yanzu kasuwa ta tashi Dankoli ya ci riba domin da tayi hakuri burinta ya cika. Yanzu tana hidimar Bautar Kasa ce wato NYSC a Kaduna sannan ta ce babu abin da ta sa a gaba yanzu illa shirin Aure.

” Da za ran Allah ya kawo mini miji Zanyi Aure. domin shine yanzu a gabana. Kafinnan kuwa zan ci gaba da yin fim dina har zuwa lokacin.”

Ta jinjina wa jarumai kamar su Ali Nuhu, Aisha Tsamiya, Abdul Shareef, da Umar Shareef, Adam Zango wanda ta ce shine sila na kai wa ga cimma burinta, da sauran ‘yan wasan finan-finan Hausa da take aiki da su.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...