Skip to main content

MATASAN ZAMFARA SUNA CIKIN WANI MAWOYACIN HALI!

MATASAN ZAMFARA SUNA CIKIN WANI MAWOYACIN HALI!

Daga; Nura mai Apple Gusau

Duk da Kasancewar Zamfara jiha ce mai Albarka kuma mai matukar tarihi. Kuma mai kima ga idanun duniya,  amma yanzu jihar Zamfara Ta zama wani bagire ko ince wana mashahurin waje na zaman banza ga matasa.  Duk da cewa gwamnatin mai girma Gwamnan jihar Zamfara wato.  (Hon,   Abdul'aziz Yari Abubakar Shattiman Zamfara)  yana iya kokarinsa kamar yadda Ake fada,  

Wannan nema dalilin da yasa yanzu inhar ankare Sallar magriba baka isa kayi yawo da babban waya a hunnunka ba. Inko kace bahaka ba yanzu ne jikinka yana gayama bayan an karbe ma waya kuma abika da sara da duka,

Ko shakka babu har zuwa yanzu haka ake cigaba da zama a wannan gari na Gusau babban birnin jihar Zamfara.  Abin tambaya anan shine shin menene yajanyo wannan al'amarin?  Zaman banza wanda shine Silar aikata wannan mummunar sana'ar.

Ana kuma cikin wannan halin sai ga Kungiyar kwadago. Ta shiga yajin aiki. Wanda shima wani babban barazana ce ga wannan gwamnati,

Muna Kira da babbar murya zuwa ga gwamnatin jihar Zamfara  da tadubi wannan matsalar da idon basira kuma ta zauna tayi karatun tanatsu domin zakulu wasu muhimman abubuwa da matasa zasu dogara da kansu.

Saboda matasa sune kaso mafi yawa daga cikin Waɗanda sunka bada tasu gudun muwa har anka kafa wannan gwamnati. Amma yanzu sun zama saniyar ware.  Domin kuwa anayi badasu ba, kuma bayan kunsan lokaci bakone. zuwa yakeyi kuma yawoce.  zuwa lokacin da Zaku dawo neman gudunmawarsu da wane ido Zaku kallesu?

Muna rokon Allah madaukakin sarki da ya bada ikon jin wannan kiran da kunnuwan basira kuma asamu gyara shine abun Alfaharin mu.  Gyara kayanka bazai taba zama dai-dai da sauke maraba ba.

Daga Nura Mai Apple Gusau.  Dan Kungiyar muryar talaka ta kasa reshen jihar Zamfara 08133376020____07086688853

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

Ta kashe Mijin ta na aure

Ta kashe Mijin ta na aure Jami'an 'Yan Sanda sun damke wata mata mai shekara 42 ta kashe Mijin ta na aure a wata Unguwa a Garin Legas. Ana zargin Folashade Idoko da kashe Mijin ta a cikin gidan su. Jaridar Daily Post tace wannan mummunan abu ya faru ne a cikin Oto-Awori na Garin Legas. Marigayin dai Injiniya ne kuma tuni dai Jamia'an 'Yan Sanda su kayi ram da wannan mata. Mai gidan hayan da Iyalin su ke yace matar wanda malamar asibiti ce ta dade su na samun matsala da Mijin na ta amma yana hakuri. Kuma dai akwai kishin-kishin din cewa kishin jaraba ne ya sa ta kashe Mijin na ta. Matar dai tace tsautsayi aka samu wuka ta fadi a jikin sa ya mutu. Jami’an tsaro sun damke wani saurayi Ifeanyi Chukwu Maxwell Dike dauke da jikin wata yarinya da aka sace a makon jiya.