Skip to main content

MATASAN ZAMFARA SUNA CIKIN WANI MAWOYACIN HALI!

MATASAN ZAMFARA SUNA CIKIN WANI MAWOYACIN HALI!

Daga; Nura mai Apple Gusau

Duk da Kasancewar Zamfara jiha ce mai Albarka kuma mai matukar tarihi. Kuma mai kima ga idanun duniya,  amma yanzu jihar Zamfara Ta zama wani bagire ko ince wana mashahurin waje na zaman banza ga matasa.  Duk da cewa gwamnatin mai girma Gwamnan jihar Zamfara wato.  (Hon,   Abdul'aziz Yari Abubakar Shattiman Zamfara)  yana iya kokarinsa kamar yadda Ake fada,  

Wannan nema dalilin da yasa yanzu inhar ankare Sallar magriba baka isa kayi yawo da babban waya a hunnunka ba. Inko kace bahaka ba yanzu ne jikinka yana gayama bayan an karbe ma waya kuma abika da sara da duka,

Ko shakka babu har zuwa yanzu haka ake cigaba da zama a wannan gari na Gusau babban birnin jihar Zamfara.  Abin tambaya anan shine shin menene yajanyo wannan al'amarin?  Zaman banza wanda shine Silar aikata wannan mummunar sana'ar.

Ana kuma cikin wannan halin sai ga Kungiyar kwadago. Ta shiga yajin aiki. Wanda shima wani babban barazana ce ga wannan gwamnati,

Muna Kira da babbar murya zuwa ga gwamnatin jihar Zamfara  da tadubi wannan matsalar da idon basira kuma ta zauna tayi karatun tanatsu domin zakulu wasu muhimman abubuwa da matasa zasu dogara da kansu.

Saboda matasa sune kaso mafi yawa daga cikin Waɗanda sunka bada tasu gudun muwa har anka kafa wannan gwamnati. Amma yanzu sun zama saniyar ware.  Domin kuwa anayi badasu ba, kuma bayan kunsan lokaci bakone. zuwa yakeyi kuma yawoce.  zuwa lokacin da Zaku dawo neman gudunmawarsu da wane ido Zaku kallesu?

Muna rokon Allah madaukakin sarki da ya bada ikon jin wannan kiran da kunnuwan basira kuma asamu gyara shine abun Alfaharin mu.  Gyara kayanka bazai taba zama dai-dai da sauke maraba ba.

Daga Nura Mai Apple Gusau.  Dan Kungiyar muryar talaka ta kasa reshen jihar Zamfara 08133376020____07086688853

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.