Skip to main content

Fassarar Jawabin Mai Girma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Wanda Ya Yi Wa Jama'ar Nijeriya A Ya'u Litinin.

Fassarar Jawabin Mai Girma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Wanda Ya Yi Wa Jama'ar Nijeriya A Ya'u Litinin.

Ya ku 'yan uwana 'yan Najeriya.

Ina mai matukar godiya ga Allah da kuma daukacin 'yan Najeriya saboda addu'o'in da suka yi mini. Ina farin cikin dawowa gida cikin 'yan uwana maza da mata.
Yayin da nake jinya a kasar Birtaniya, ina samun labaran abubuwan da ke faruwa a gida.

'Yan Najeriya suna tattauna al'amuran da suke faruwa, amma na fahimci cewa wasu daga cikin kalaman da ake yi musamman a kafofin sada zumunta sun ketara iyakar dokokin kasar nan inda suke sanya alamar tambaya game da ci gaba da kasancewarmu a matsayin kasa guda. Wannan wani abu ne na wuce gona da iri.

A shekarar 2003 bayan da na shiga siyasa, marigayi Cif Emeka Ojukwu ya taba ziyarta ta kuma ya zauna wurina a Daura.

Mun kwashe fiye da kwana biyu muna tattauna matsalolin Najeriya, a wasu lokutan mukan shafe dare muna magana. A karshe mun cimma matsayar cewa wajibi ne Najeriya ta ci gaba da kasancewa kasa daya kuma dunkulalliyya.

Hadin kan 'yan Najeriya wani abu ne da aka cimma matsaya a kai. Kuma ba ya bukatar a sake waiwayarsa.

Ba za mu bari wasu marasa dattako su fara tada fitina kuma idan abubuwa suka lalace su gudu su bar wasu da aikin dawo da doka da oda, wata kila ma hakan ba zai yiwu ba sai an zub da jini.
Kowane dan Najeriya yana da 'yancin rayuwa da kuma gudanar da harkokinsa a ko ina a Najeriya ba tare da an yi masa wani shamaki ba.

Na yi amannar cewa dimbin 'yan Najeriya suna da irin wannan tunani.
Sai dai wannan ba yana nufin cewa babu kwararan batutuwan da suke damun mu ba.

Kowane bangare yana da korafinsa. Amma dadin tsarin da ake tafiyar da kasar a kai yanzu shi ne, yadda ya tanadin hanyoyin da duk wadanda suke ganin an yi musu ba daidai ba, za su iya gabatar da korafinsu da kuma yadda za a ci gaba da tafiya tare.

Majalisar dokoki ta kasa da kuma majalisar koli ta kasa su ne wuraren da doka ta yarda a tattauna manyan batutuwan da suka shafi Najeriya.

Baki ya zo daya a kasa baki daya cewa ya fi kamata a ci gaba da zama tare maimakon a raba kasar.
Bugu da kari, ina kira da rundunonin tsaro da kada nasarar da aka samun a watanni 18 da suka gabata ta sa su, su rage kaimi.
Wajibi ne mu yaki 'yan ta'adda da miyagu kuma mu ga bayansu saboda mu ci gaba da rayuwa cikin zaman lafiya da tsaro.

Wannan ya sa za mu kara kaimi ba kawai a yaki da 'yan Boko Haram ba wadanda suka fito da sabbin hanyoyin kai wa mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba hari.
Hakazalika za mu sa kaimi a yaki da masu satar mutane don neman kudin fansa da rikicin Fulani makiyaya da manoma da rikicin kabilanci wanda wasu 'yan siyasa masu munanan manufa suke rura wutarsa. Za mu magance su duka.

A karshe 'yan uwana 'yan Najeriya abin da ya dace yanzu shi ne mu manta da bambance-bambancen da ke tsakaninmu, mu fuskanci wadannan kalubalen da suka shafe mu duka; wato gyara tattalin arziki da bunkasar siyasa da hadin kan kasa, har ila yau, da samar wa 'yan Najeriya dawwamanman zaman lafiya.

A shirye nake don ganin mun cimma wannan burin da kuma ganin dorewarsu. Ina farin cikin dawowa gida.

Na gode kuma Allah Ya albarkaci kasarmu.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...