Skip to main content

Fassarar Jawabin Mai Girma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Wanda Ya Yi Wa Jama'ar Nijeriya A Ya'u Litinin.

Fassarar Jawabin Mai Girma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Wanda Ya Yi Wa Jama'ar Nijeriya A Ya'u Litinin.

Ya ku 'yan uwana 'yan Najeriya.

Ina mai matukar godiya ga Allah da kuma daukacin 'yan Najeriya saboda addu'o'in da suka yi mini. Ina farin cikin dawowa gida cikin 'yan uwana maza da mata.
Yayin da nake jinya a kasar Birtaniya, ina samun labaran abubuwan da ke faruwa a gida.

'Yan Najeriya suna tattauna al'amuran da suke faruwa, amma na fahimci cewa wasu daga cikin kalaman da ake yi musamman a kafofin sada zumunta sun ketara iyakar dokokin kasar nan inda suke sanya alamar tambaya game da ci gaba da kasancewarmu a matsayin kasa guda. Wannan wani abu ne na wuce gona da iri.

A shekarar 2003 bayan da na shiga siyasa, marigayi Cif Emeka Ojukwu ya taba ziyarta ta kuma ya zauna wurina a Daura.

Mun kwashe fiye da kwana biyu muna tattauna matsalolin Najeriya, a wasu lokutan mukan shafe dare muna magana. A karshe mun cimma matsayar cewa wajibi ne Najeriya ta ci gaba da kasancewa kasa daya kuma dunkulalliyya.

Hadin kan 'yan Najeriya wani abu ne da aka cimma matsaya a kai. Kuma ba ya bukatar a sake waiwayarsa.

Ba za mu bari wasu marasa dattako su fara tada fitina kuma idan abubuwa suka lalace su gudu su bar wasu da aikin dawo da doka da oda, wata kila ma hakan ba zai yiwu ba sai an zub da jini.
Kowane dan Najeriya yana da 'yancin rayuwa da kuma gudanar da harkokinsa a ko ina a Najeriya ba tare da an yi masa wani shamaki ba.

Na yi amannar cewa dimbin 'yan Najeriya suna da irin wannan tunani.
Sai dai wannan ba yana nufin cewa babu kwararan batutuwan da suke damun mu ba.

Kowane bangare yana da korafinsa. Amma dadin tsarin da ake tafiyar da kasar a kai yanzu shi ne, yadda ya tanadin hanyoyin da duk wadanda suke ganin an yi musu ba daidai ba, za su iya gabatar da korafinsu da kuma yadda za a ci gaba da tafiya tare.

Majalisar dokoki ta kasa da kuma majalisar koli ta kasa su ne wuraren da doka ta yarda a tattauna manyan batutuwan da suka shafi Najeriya.

Baki ya zo daya a kasa baki daya cewa ya fi kamata a ci gaba da zama tare maimakon a raba kasar.
Bugu da kari, ina kira da rundunonin tsaro da kada nasarar da aka samun a watanni 18 da suka gabata ta sa su, su rage kaimi.
Wajibi ne mu yaki 'yan ta'adda da miyagu kuma mu ga bayansu saboda mu ci gaba da rayuwa cikin zaman lafiya da tsaro.

Wannan ya sa za mu kara kaimi ba kawai a yaki da 'yan Boko Haram ba wadanda suka fito da sabbin hanyoyin kai wa mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba hari.
Hakazalika za mu sa kaimi a yaki da masu satar mutane don neman kudin fansa da rikicin Fulani makiyaya da manoma da rikicin kabilanci wanda wasu 'yan siyasa masu munanan manufa suke rura wutarsa. Za mu magance su duka.

A karshe 'yan uwana 'yan Najeriya abin da ya dace yanzu shi ne mu manta da bambance-bambancen da ke tsakaninmu, mu fuskanci wadannan kalubalen da suka shafe mu duka; wato gyara tattalin arziki da bunkasar siyasa da hadin kan kasa, har ila yau, da samar wa 'yan Najeriya dawwamanman zaman lafiya.

A shirye nake don ganin mun cimma wannan burin da kuma ganin dorewarsu. Ina farin cikin dawowa gida.

Na gode kuma Allah Ya albarkaci kasarmu.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020