Skip to main content

KUNGIYAR STUDENT ALLIANCE SUPPORT OF BELLO MUHAMMAD MATAWALLE (SA-BELMAT)

KUNGIYAR STUDENT

tayi zama yau daya daga cikin wadanda suka kirkiro da wannan kungiya wato Comrade Umar Mahmud Umar, ya ce; "babban makasudin zaman shine munga ya dace mu fito a matsayinmu na 'yan jiha, kuma a matsayinmu na wani yanki daga cikin daliban jihar Zamfara muyi godiya ta musamman bisa ga irin gwaggwarmaya da chanji da Hon Luqman Majidadi ya kawo karkashin jagorancin mai girma gwamnan jihar Zamfara na bashi wannan jagorancin, da kuma shi gwamna a bisa babban aikin da ya dauko wajan ganin a samu ilimi a cikin jihar Zamfara".

Ya ce; "kamar yadda muka sani akwai dalibai wajan 700 daga jihar zamfara wadanda aka dauko kuma aka tantance mutum 200 daga ciki zasu je suyi karatun a bangare daban-daban tun daga abinda ya shafi bangare tiyata da kuma hada magunguna da sauransu, wanda insha Allahu nan da shekaru zuwa goma zamu samu 'yan asalin  jihar Zamafar da suka samu kwarewar da zasu ci gaba da kula da 'yan uwansu a cikin kauyuka da kuma biranen jihar Zamfara, wanda in aka dubi tun inda aka fito shekara goma ba'a taba samun gwamnatin da tazo cikin lokaci daya ta daukin nauyin dalibai sama da 200 ba, ko kuma wani abu mai kama da haka, sai a karkashin jagorancin wannan gwamna, to shi yasa muka ga ya kamata muzo mu bayyanawa duniya jin dadinmu a bisa irin wannan namijin kokari da ake yi".

Yace; "kamar yadda kuke gani irin namijin kokarin da shugaban daliban jihar Zamfara wato (Hon, Kuqman majidadi keyi, tun daga wajan tantance dalibai, hadi da samar masu da tikiti da kula dasu da samar masu da muhali  mai kyau a  kasashen ketare  abun yabawa ne". Yace; zuwan Majidadin, ke da wuya a ofis ya dukufa wajan ziyarce-ziyarce a wasu manyan jami'o'in kasar nan, domin yin bincike akan shin wane bashi ne waccan tsohuwar gwamnati ta bari wanda su yanzu zasu dubi kokarin da ya kamata suyi, saboda akwai daliban jihar Zamfara masu karatu Al'hikima har yanzu basu karbi dakardunsu ba, akwai wasu an kaisu sunyi karatu a kasar India biyan kudin ya gagara, to wannan ba karamin kokarin bane" a cewar Comrade Umar.

Haka ya kara da cewar "kungiyar (Sa-Belmat) tun lokacin da aka kirkireta ta samar da ayyukanyi ga matasa". A karshe yayi godiya ga gwamna Bello Muhammad Matawalle akan rakiyar da yayi wajan ganin cewa an wayar da kan jama'a kan cin hanci da rashawa. Haka yayi addu'ar samun zaman lafiya da arziki mai albarka a jihar Zamfara da Najeriya baki daya.

Sharhi;

munyi jinjina sosai da wannan kungiya idan maka dubi irin kokarinta wajan samar da cigaba ga matasa, muna fatan gwamnatin gwamna Bello Muhammad Matawalle zata kara kaini domin ganin matasan jihar Zamfara sun samu ilimi mai nagarta wanda zai taimaki jihar nan ta kowane bangare

Daga Nura Muhamad Mai Apple Gusau

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...