Skip to main content

Masu Neman Shugabancin PDP Zasu Rattaba Hannu A Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Ranar Talata – Inji Dokpesi






Jigo a jam’iyyar adawa ta PDP, Cif Raymond Dokpesi kuma daya daga cikin ‘yan takarar neman shugabancin jam’iyyar, ya ce dukkanin masu neman takara su 8 za su rattaba hannu a yarjejeniyar zaman lafiya a matsayin wani ɓangare na samun nasara a babban taron da za a yi a watan Disamba.

Dokpei, wanda ya kafa kamfanin Daar Communications, ya bayyana wannan a cikin wata hira da manema labarai bayan taro inda kungiyar gwamnonin PDP ta gana da dukan masu neman takara a Enugu, wanda aka kammala a safiyar yau Litinin.

Kamar yadda majiyar mu, ke da labari , Dokpesi ya bayyana cewa duk masu neman takara sun amince da su shiga yarjejeniyar zaman lafiya a babban sakatariyar jam’iyyar, Wadata Plaza, wanda ke birnin Abuja a daidai karfe 4 na yamma.

Ya ce ‘yan takara sun amince suyi aiki tare.

Gwamnan jihar Ekiti kuma shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Mista Ayodele Fayose ya bayyana cewa taron koli na kasa, wanda za a gudanar a ranar 9 ga watan Disamba, zai zama wata abin koyi ga sauran jam’iyyun siyasa.

Wadanda suka halarci taron sun hada da shugaban jam’iyyar, sanata Ahmed Makarfi da duk gwamnonin PDP sun halarci taron, sai dai gwamnan jihar Ebonyi ya tura wakilinsa.

Sauran masu neman shugabancin PDP a taron sune, Cif Bode George, Gbenga Daniel, Prince Uche Secondus, Farfesa Tunde Adeniran, Jimi Agbaje, Taoheed Adedoja da kuma Rashid Ladoja.

Cikin wadanda suka kuma halarci taron, sun hada da Ike Ekweremadu, mataimakin shugaban majalisar dattawa da Gabriel Susuwan, tsohon gwamnan jihar Binuwai da Adolphus Nwabara da kuma Sule Lamido.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...