Skip to main content

Kira ga Hukumar Sadarwa ta kasa


Kamar yadda hukumar sadarwa ta bayar da wa'adin kammala haɗe layin waya da kuma numbobin katin zama ɗan ƙasa, wanda kuma yanzu haka mutane na ci gaba da yin tururuwa wajen ofisoshin da ake yin katin na zama ɗan ƙasa, akwai bukatar hukumar dake yin wannan katin na zama ɗan kasa ta kara yilwata ofisoshin yin aikin, domin taƙaita wahala ga al'umma, wajan samun damar mallakar rijistar da milyoyin mutanen da basu samu damar yin rijistar ba suke fafutikar ganin sun samu.


Dubban mutanen dake tururuwa wajen inda ake yin rijistar suna galabaita matuƙa. Wasunsu duk irin yanayin sanyin da ake fama da shi, amma a haka suke bacci a wajen, domin ganin sun mallaki katin. Wanda hakan yake janyo turmutsutsu, wasu lokutan har da faɗace-faɗace, kuma hakan yana faruwa ne sanadiyar rashin samun wadatattun wuraren da ake gudanar da aikin. 


Saboda haka ya kamata wannan hukuma ta dubi yiwuwar kara wajajen gudanar da waɗannan ayyukan, domin ganin 'yan kasa waɗanda basu mallaki katin ba, sun samu damar yinsa ba tare da shan wahala sosai ba. Duk da munsan hukumar tayi namijin ƙoƙari na irin tsawon lokacin da ta dauka tana gudanar da wannan aiki a cikin ƙasa.

Ko ba komai haɗewar layin waya (Sim Card) da kuma katin zama ɗan ƙasa( NIN) yana da matuƙar muhimmancin gaske, domin dukkansu abubuwa ne da suke tattare da dukkan bayanai na mutum, wanda kuma idon aka samu nasarar wannan aiki, hakan zai taimaka wajen samar da tsaro a cikin kasa, domin duk wanda ya san akwai bayanansa a hukumance da wahala ya aikata wani babban laifin da zaisa farautarsa.


Muna fatan Allah ya kawo mana zaman lafiya madauwami a Najeriya, ya bamu haɗin kai da kaunar juna. Ya karo mana arziki mai albarka.


Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020