Skip to main content

Kira ga Hukumar Sadarwa ta kasa


Kamar yadda hukumar sadarwa ta bayar da wa'adin kammala haɗe layin waya da kuma numbobin katin zama ɗan ƙasa, wanda kuma yanzu haka mutane na ci gaba da yin tururuwa wajen ofisoshin da ake yin katin na zama ɗan ƙasa, akwai bukatar hukumar dake yin wannan katin na zama ɗan kasa ta kara yilwata ofisoshin yin aikin, domin taƙaita wahala ga al'umma, wajan samun damar mallakar rijistar da milyoyin mutanen da basu samu damar yin rijistar ba suke fafutikar ganin sun samu.


Dubban mutanen dake tururuwa wajen inda ake yin rijistar suna galabaita matuƙa. Wasunsu duk irin yanayin sanyin da ake fama da shi, amma a haka suke bacci a wajen, domin ganin sun mallaki katin. Wanda hakan yake janyo turmutsutsu, wasu lokutan har da faɗace-faɗace, kuma hakan yana faruwa ne sanadiyar rashin samun wadatattun wuraren da ake gudanar da aikin. 


Saboda haka ya kamata wannan hukuma ta dubi yiwuwar kara wajajen gudanar da waɗannan ayyukan, domin ganin 'yan kasa waɗanda basu mallaki katin ba, sun samu damar yinsa ba tare da shan wahala sosai ba. Duk da munsan hukumar tayi namijin ƙoƙari na irin tsawon lokacin da ta dauka tana gudanar da wannan aiki a cikin ƙasa.

Ko ba komai haɗewar layin waya (Sim Card) da kuma katin zama ɗan ƙasa( NIN) yana da matuƙar muhimmancin gaske, domin dukkansu abubuwa ne da suke tattare da dukkan bayanai na mutum, wanda kuma idon aka samu nasarar wannan aiki, hakan zai taimaka wajen samar da tsaro a cikin kasa, domin duk wanda ya san akwai bayanansa a hukumance da wahala ya aikata wani babban laifin da zaisa farautarsa.


Muna fatan Allah ya kawo mana zaman lafiya madauwami a Najeriya, ya bamu haɗin kai da kaunar juna. Ya karo mana arziki mai albarka.


Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.