Skip to main content

Yazeed Trust Fund, Yazeed Network




A ranar Assabar 11/07/2020 wasu daga cikin tawagar jajirtattun kungiyoyin mata 21 sun ka dubi dacewar bayar da lambar yabo ta girmamawa ga Hajiya Aliya Saraki sarakin Yazeed, shugabar kungiyar Yazeed Network. Bayar da wannan kyauta dai na nufin kara mata kwarin gwiwar tashi tsaye wajan kara tanke damarar gwagwarmayar cigaban al'umma.



Mai Apple wakili ne, a wasu kafafen watsa labarai daban-daban a kafofin sadarwa daban-daban, ya ziyarci wajan a lokacin bikin karramawar kuma ya kalato mana bayanai daban-daban mabambanta. Kamar yadda zakuji.



Kungiyoyin matan 21 wasu da dama daga cikinsu sun samu damar lekawa a wajan bikin. Inda bukin ya samu halartar mutane da dama, wasu daga cikinsu harda jami'an tsaro, da 'yan siyasa, da mawaka. Bikin wanda mafi yawa mata ne, domin su suke da ruwa da tsakki a wajan.

Bikin karramawar ya gudana ne a Nafirst Hotel dake shiyar samaru a Gusau babban birnin jihar Zamfara.




Wata da muka sakaya sunanta saboda wasu dalilai, a cikin jawabinta ta ce; sun dubi yiwuwar karrama Hajiya Aliya ne saboda kokarinta a cikin tafiyar Alh Yazeed Shehu Danfulani Mai Doya.

Shugabar Mata ta Gidauniyar Yazeed Trust Fund hajiya Maryam Danfuloti, a cikin jawaban nata tayi matukar nuna farin cikinta, a bisa wannan abun alheri, inda tace tana alfahari da duk wani abun ci gaba da za'a samar a karkashin jagorancinta, saboda haka wannan babban abun yabawa ne.

Daya bangaran Shugaban amintattu na tafiyar Alh Yazeed Shehu Danfulani, kuma shugaban Gidauniyar Yazeed Trust Fund Comrade Rufa'i Bala U&B salanken Galadima, shima ya tofa albarkacin bakinsa, sannan ya yi nuni da cewa kowane lokaci tafiyar Yazeed cike take da gagarumar nasara, inda a karshe yayi addu'ar Allah ya sa kowa ya koma gida lafiya.

A wajan taron wakilinmu ya shedar da ganin wasu daga cikin fuskokin 'yan fafutikar tafiyar gidan Alh Yazeed Shehu Danfulani. Wadanda suka hada da;

Hajiya Maryam Danfuloti
Hajiya Aisha 'yar Asali
Hajiya Mai Glass
Comrade UB Shugaba
Abdurrahaman
zayyanu Dan Mamman
Maikaji Sarkin Yakin Yazeed
Basheer Isiya Figo
Kaura Namadina kauran Yazeed




da sauran mutane da dama.

A lokacin jawabin nata Sarakin ta nuna matukar farin cikinta, a bisa wannan karamci da aka nuna mata, da kuma dubin cancantarta hadi da dogon nazarin bata wannan lambar yabo ta girmamawa. Sannan tayi addu'a ga 'yan uwa da abokan arziki hadi da masu yi mata fatan alheri da sun ka samu damar karba wannan goron gayyatar. Hadi da addu'ar Allah ya kara dafawa Alh Yazeed Shehu Danfulani, domin kara  ci gaba da taimakon marasa galihu.

Mai Apple Media Reporter

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...