Skip to main content

SHUGABAR YAZEED NETWORK TA KARBI TAWAGAR MANYAN KUNGIYOYIN MATA DOMIN NUNA GOYON BAYA WAJAN CI GABAN AL'UMMA





Kungiyar Yazeed Network wanda Hajiya Aliya Saraki ke shugabanta, ta karbi tawagar wasu ayarin kungiyoyin Mata domin marawa tafiyar (Alh  Yazeed Shehu Danfulani baya, wannan karbar na zuwa  ne a daidai lokacin da ayyukan alheri ke ci gaba da sauka a cikin al'umma ta hannun Alh Yazeed Shehu Danfulani,

Wadannan kungiyoyi sunyi la'akari da muhimmancin dake akwai wajan irin amfanin al'umma, musamman zuwa ga marasa galihu masu kokarin ganin sun dogara da kansu, a lokacin karbar wannan tawagar an gudanar da jawabai da dama mabambanta wasu daga cikinsu shine, shuwagabannin
wadannan kungiyoyi sun nuna farin cikinsu  matuka da gaske a kan irin yadda wannan bawan Allah ya himmatu wajan ganin marayu da marasa karfi sun amfana a cikin arzikin da Allah yayi masa.

A lokacin jawabin godiya wanda shugabar wannan kungiya ta Yazeed Network Hajiya Aliya saraki tayi matukar nuna farin cikinta a bisa wannan dogon nazari da wadannan bayin Allah su kayi wajan zuwa a hada hannu da karfe wajan ci gaba da ayyukan alheri a cikin al'umma, cikin jawabin nata wanda ta fi mayar da hankali kan irin kyakkyawan yanayi da aka samu na zimmar ganin Alh Yazeed Ya yi amfani da abinda yake da shi wajan ganin marasa galihu sun samu fita daga cikin kangin da suke ciki,  kuma tayi kira ga masu hannu da shuni a cikin al'umma domin suyi koyi da irin halayyar Alh Yazeed Wajan aikin tawali'u a cikin al'umma.

A cikin jawabin shugabar tayi jinjina ga mata sannan tayi jinjina ga dukkan magoya bayan Alh Yazeed Shehu Danfulani, haka tayi kira ga matan da suka dubi yiyuwar bin wannan tafiya da su jajirce domin ko ba komai an san mata da jajircewa ga abinda ya shafi harkar sa kai, a karshe tayi addu'ar samun dukkan nasara tare da fatan watsewa lafiya.

A dayan bangare limamin kawo sauyi mai ma'ana a cikin al'umma, kuma shugaban gwagwarmayar Alh Yazeed Shehu Danfulani, wato Comrade Rufa'i Bala UB Gusau, yayi dan takaitaccen jawabi,  sannan ya nemi hadin kai da goyon baya domin nasarar tafiyar.

Idan dai zamu ita tunawa ko in ce idan muna biye sau da kafa zamu kasance cikin  wasu daga cikin wadanda suka shedi ayyukan alherin wannan bawan Allah na zahiri, kama tun daga daukar nauyin yara zuwa makarantu hadi da daukar nauyin dawayniyarsu, domin ganin suma sun kasance abun moriya a cikin al'umma. Haka mun shedi irin yadda yake taimakon al'umma ta bangaren samar da ruwan sha, hadi da gyaran masallatai da bayar da tallafi a asibitoci da sauran ayyukan da lokaci ba ba zai bamu damar zaiyanuwa ba.

a nan  muna amfani da wannan damar domin addu'ar samun dukkanin nasara ga tafiyar Alh Yazeed Shehu Danfulani, kasancewarsa mutum mai son ci gaban al'umma.

Rahoto, Daga Nura Mai Apple,  Media Reporter Zamfara Najeriya.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...