Skip to main content

KUNGIYAR YAZEED NETWORK TA KARBI KUNGIYOYIN MATA 7

wasu daga cikin kungiyoyin mata

                    ceo founder Yazeed Network

Yazeed Network kungiya ce da aka assasa kuma aka bude ta domin tafiya kafada-da-kafada da sauran kungiyoyin dake fafutikar ilmantar da al'umma, hadi da wayar da kan al'umma akan manufofi hadi da bayyana alherai na (Alh Yazeed Shehu Danfulani Mai Doya), wadanda yake yi ga al'umma.

Wata jigo daga cikin babbar kungiyar Yazeed Trust Fund ce ta kirkiri kungiyar, domin hada karfi da karfe, wajan wannan gwagwarmaya. Hajiya Aliya Saraki, ita ce shugabar Kungiyar Yazeed Network.

A kokarin kungiyar na ganin ta zakulo kungiyoyin mata a sassa daban-daban na jihar Zamfara, a Ranar alhamis din da ta gabata ta karbi wasu gungun kungiyoyin mata 7 wadanda suka jaddada goyon bayansu ga tafiyar (Alh Yazeed Shehu Danfulani Garkuwan Matasan Gusau Lamidon Tsafe).

Jawabin shugabar kungiyar a yayin taron ta jinjina wa tawagar wadannan kungiyoyi tare da shan alwashin hada karbi tare da su domin aiki tukuru wajan samun kowace irin nasara da ake bukata.

Sarakin, ta jinjina wa (Alh Yazeed Shehu Danfulani a bisa kyawawan manufofinsa a kan al'ummarsa tare da bayar da tabbacin wadannan manufofi za su ci gaba da gudana cikin iyawar Allah. A karshe tayi addu'ar Allah ya sakawa wadannan kungiyoyi da mafificin alheri.

Jawaban da suka gabatar shuwagabannin wadannan kungiyoyi sun nuna farin cikinsu akan irin yadda aka tarbesu hannuwa biyu, duba da ganin suma akwai rawar da suke iya takawa wajan ci gaba da yaɗa manufofin Yazeed.

Daya gefen Shugaban gudanarwa na Tafiyar Yazeed Trust Fund. (Comrade Rufa'i Bala UB Gusau),
a nasa jawabin ya taba muhimman batutuwa, daga ciki yana cewar, duk da kasancewar (Alh Yazeed Shehu Danfulani) baya rike da wata kujerar siyasa a Jihar Zamfara, to amma irin ayyukan da yakeyi don Al'umma abun koyi ne. Ya ce; wani babban abun farin ciki shine yadda  '' Yara Masu Daraja'' ne gaban (Alh Yazeed Shehu Danfulani).

taron ya gudana, kuma ya kammala cikin ƙoshin lafiya. A cikin taron akwai abokanin  aiki waɗanda suka tsakaya domin jajircewar samun cikakkiyar nasara.



Rahoto; Daga Nura Mai Apple. Media Reporter 08133376020


Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020