Skip to main content

MATAKAN DA SHUGABAN KASAR CHADI YA DAUKA SUN DACE!





Fannin samar da tsari, walwala hadi da jin dadin al'umma, wannan babban nauyi wanda ya rataya a wuyan kowane shugaba halatacce, wanda al'umma sun ka zaɓa da zimmar inganta rayuwarsu ta fannoni da dama. Demokaradiyya a siyasance tsari ne wanda aka fito da shi domin shugabannin duniya su saki mara ga talakawansu, su samar masu da kayayyakin more rayuwa, kama tun daga, inganta tsaro, wadata kasa da abinci, samar da hanyoyi, samar da wutar lantarki, samar da ilimi, samar da ruwan sha, da kuma fannin lafiya._
_Babu wata kasa a duniya da zata ci gaba matukar babu waɗannan. Babban abun nema ruwa-ajallo shi ne; tsaro, domin sai da shine sannan komai zai gudana cikin jin dadi da walwala.


Mun ya ba matuƙa ga irin yadda shugaban kasar Chadi Idris Daby yake kokarin ganin ya tsame kasarsa daga cikin jerin kasashen dake fama da safgar ta'addanci, ko shakka babu wannan shugaba yayi abun yabawa idan mukayi la'akari da yadda shugaban ya zage damtse, an ka fita da shi filin daga domin yaki da 'yan ta'adda waɗanda sun ka zama ƙarfen ƙafa a cikin yankunan ƙasashen dake kewaye da tafkin Chadi.


Wannan nasara da zaratan sojojin kasarsa suka samu abin murna ne, kuma hakan wata manuniya ce dake nuna shugaban kasar da gaske yake wajan fito-na-fito da 'yan kungiyar mayakan Boko Haram, masu kokarin ganin sun kassara waɗannan kasashe namu masu albarka.


Kan abin da ya shafi wannan yaki, ko shakka babu bai kamata abar shugaban kasar Chadi da wannan gumurzo shi kaɗai ba, akwai buƙatar kasashen Najeriya da Nijar da Kamaru su taimaka masa, domin ganin an samu nasarar wannan yaki, kasancewar dukkan wadannan kasashen suna fama da matsalolin tsaro haiƙan!


Idan sauran kasashen da ke kewaye da wannan yanki sun ka fito kamar yadda Shugaba Idris Daby ya fito an kayi hadaka ta musamman wadda ba sani ba sabo, insha Allahu da karfin Allah za'a samu nasarar kawo karshen wannan al'amari wanda yasa da yawa daga cikin dubban mutane sun ka rasa rayukansu, wasu da dama sun ka rasa muhallansu, da dama daga cikin wasu sun ka rasa abin da zasu ci ta sanadiyar wannan kalubale, shekaru da dama da suka gabata.


Faɗa irin wannan mai cike da hatsari akwai buƙatar a cire son zuciya a haɗu a bisa manufa daya, domin samun nasara, kasancewar yaƙi ɗan zamba ne, kowace ƙasa akwai irin nata gudunmuwar da zata iya bayarwa ta fuskoki da dama.


Kalaman shugaban kasar ta Chadi da ya furta na cewar dakarun Ƙasarsa, ba zasu kara fita kasar ba, da zimmar taimakon wata kasa, sai dai su tsaya su tsare Ƙasar ta su, domin ganin sun kakkaɓe kasar daga ƙangi na tsaro, ƙura ce ta kai bango, to sai dai kuma wannan wata manuniya ce ga kasashen da wannan lamari ya shafa. Muna fatan dai zai mayar da wuƙarsa kube, ya samu haɗin kan sauran kasashen yankin dake keyawa da Tafkin na Chadi, don haɗa gwiwa domin ganin an samu kaiwa ga nasara.

A karshe muna addu'ar Allah ya kawo mana karshen wannan lamari da ya daɗe yana ciwa al'umma tuwo a kwarya, Allah ya kawo mana lafiya da zama lafiya da arziki mai albarka a kasashenmu na Afrika dama duniya baki daya, zaman lafiya ya fi zama dan sarki. Nagode!


Daga Nura Mai Apple,  Shugaban Ƙungiyar Matasa 'Yan Gwagwarmaya.




Copyright©maiapple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.