Skip to main content

HALAYYAR KIRKI SABO! Daga majalisar Himma Shayi.




Yana daga cikin cikar kamilin ɗan Adam cika alƙawari, yunkurin Gidauniyar (Alh, Yazeed Shehu Ɗanfulani Mai Doya), wajan ganin al'umma sun samu na kansu. Wannan Gidauniya ta samu damar komawa a majalisar Himma Shayi, domin cika alƙawarin da ta ɗauka a siyan sabon injinin yin faci sabo fin ga shugaban wannan ƙungiya ta majalisar himma, dake a mazauni wajan gidan man mai Littafai dake daura da kasuwar kanawa a nan cikin Tudan wada, Gusau babban birnin jihar Zamfara.


Idan dai masu karatu suna biye da mu a cikin wannan makon ne mai ƙarewa wannan Gidauniya ta samu zuwa wannan majalisa ta Himma shayi, in da ta ƙaddamar da Forms ga (Yara Masu Daraja) marayu da kuma marasa galihu a cikin al'umma, 20 da zimmar daukar nauyinsu zuwa makaranta, don bayar da tashi gudunmuwa ta fuskar ilimi abun nema!

A lokacin da gidauniyar Yazeed Trust Fund ta ziyarci majalisar Himma shayi  wajan ƙaddamar da wannan forms ta lura sosai shugaban majalisar wanda kuma shine mai yin sana'r Faci a wajan, injinin da yake amfani da shi wajan daukar nauyin iyalansa ya tsufa sosai, wanda hakan kan kawo masa cikas wajan neman abun sawa ga bakin salati. Gidauniyar ta lashi takobin kawo masa sabon injin domin yayi amfani da shi wajan daukar ɗawainiyar iyalinsa.


A cikin jawabin limamin tafiyar Gidauniyar (Alh Yazeed Shehu Ɗanfulani Mai Doya Garkuwan Matasan Gusau, Lamiɗon Tsafe) wato (Comrade Rufa'i Bala UB Salanken Galadima) ya taɓo muhimman abubuwa inda da farko ya fara sallama sannan ya ci gaba da jawabinsa kamar haka; "Alhamdulillahi a bisa alƙawarin da mu kayi na bayar da wannan tallafi a wannan majalisa  ba muyi ƙasa a gwiwa ba, mun zo domin cika wannan alƙawari, ga wannan shugaban majalisa a matsayin yana uba dattijo kuma shugaba a wannan majalisa sama da shekaru 20 da suka gabata, kuma wannan majalisa ba'a taɓa kamata da wani laifi ba a hukumance, majalisa ce wadda ta tara al'umma mabambanta kamar 'yan siyasa, jinin sarauta, dattijai, matasa, da sauran al'umma".

"saboda haka mun ka dawo wannan majalisar domin cika wannan alƙawari da muka dauka, kasancewar muna da damar yin haka.  saboda haka cike da fatan wannan Genaretor da muka damƙa maka, Allah ya sanya albarka da alheri a ciki, ya sa nan da shekara mai zuwa kaima ka baiwa wani".

A ƙarshe ya godewa wannan majalisar da kuma al'ummar da wannan majalisa ta tara, a bisa wannan gagarumar tarbo da aka samu daga wannan waje, tun daga karramawa da shayi na gaske, da kuma shimfiɗar fuska.

Haka a lokacin da aka bayar da turun magana ga shugaban majalisar ya nuna matuƙar farin cikinsa a bisa wannan namijin ƙoƙari, na bashi wannan abun neman abinci, sannan yayi kira ga sauran 'yan siyasa da masu hannu da shuni da suyi ko'i da halayyar Yazeed wajan taimakon al'umma gwargwadon hali. A ƙarshe yayi addu'ar Allah ya saka masa da mafificin alhari.

A lokacin bayar da wannan kyauta na lura sosai, da bayanai da wani jigo daga cikin dattawan majalisar yayi na cewa, basu  da abinda zasu iya cewa ga Yazeed sai dai fatan alheri, domin ya yi masu halacci da karamci a lokacin suka isa jihar Kaduna wajan gudanar da wasu ayyuka, Allah ya ƙaddara sun kayi kicibis da wajan saukar baƙi na (Alh Yazeed Shehu Ɗanfulani) a jihar  Kaduna, duk da kasancewar su basu san wannan waje na ɗan Zamfara ne ba, amma da Yazeed yaji ance 'yan Zamfara ne, nan take aka shigar da su wannan waje, kuma suka zauna a ciki, har tsawun lokaci da sun ka buƙaci komawa gida. Yace wani babban abun burgewa shine irin yadda wajan an rarraba shi ɓangare-ɓangare kuma an rubuta sunayen wasu daga cikin sunayen sassan jihar Zamfara.

Bayan kammala nashi jawabin wasu da dama sun gabatar da nasu jawaban, daga karshe sunyi addu'a da fatan alheri ga wannan tafiya mai cike da alheri.


Daga yanzu Kowane lokaci, al'ummar majalisar Himma Shayi  A Shirye Suke su bada tasu gudunmuwa, idan buƙatar hakan ta samu!

Daga Nura Mai Apple Media Reporter.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020