Skip to main content

HALAYYAR KIRKI SABO! Daga majalisar Himma Shayi.




Yana daga cikin cikar kamilin ɗan Adam cika alƙawari, yunkurin Gidauniyar (Alh, Yazeed Shehu Ɗanfulani Mai Doya), wajan ganin al'umma sun samu na kansu. Wannan Gidauniya ta samu damar komawa a majalisar Himma Shayi, domin cika alƙawarin da ta ɗauka a siyan sabon injinin yin faci sabo fin ga shugaban wannan ƙungiya ta majalisar himma, dake a mazauni wajan gidan man mai Littafai dake daura da kasuwar kanawa a nan cikin Tudan wada, Gusau babban birnin jihar Zamfara.


Idan dai masu karatu suna biye da mu a cikin wannan makon ne mai ƙarewa wannan Gidauniya ta samu zuwa wannan majalisa ta Himma shayi, in da ta ƙaddamar da Forms ga (Yara Masu Daraja) marayu da kuma marasa galihu a cikin al'umma, 20 da zimmar daukar nauyinsu zuwa makaranta, don bayar da tashi gudunmuwa ta fuskar ilimi abun nema!

A lokacin da gidauniyar Yazeed Trust Fund ta ziyarci majalisar Himma shayi  wajan ƙaddamar da wannan forms ta lura sosai shugaban majalisar wanda kuma shine mai yin sana'r Faci a wajan, injinin da yake amfani da shi wajan daukar nauyin iyalansa ya tsufa sosai, wanda hakan kan kawo masa cikas wajan neman abun sawa ga bakin salati. Gidauniyar ta lashi takobin kawo masa sabon injin domin yayi amfani da shi wajan daukar ɗawainiyar iyalinsa.


A cikin jawabin limamin tafiyar Gidauniyar (Alh Yazeed Shehu Ɗanfulani Mai Doya Garkuwan Matasan Gusau, Lamiɗon Tsafe) wato (Comrade Rufa'i Bala UB Salanken Galadima) ya taɓo muhimman abubuwa inda da farko ya fara sallama sannan ya ci gaba da jawabinsa kamar haka; "Alhamdulillahi a bisa alƙawarin da mu kayi na bayar da wannan tallafi a wannan majalisa  ba muyi ƙasa a gwiwa ba, mun zo domin cika wannan alƙawari, ga wannan shugaban majalisa a matsayin yana uba dattijo kuma shugaba a wannan majalisa sama da shekaru 20 da suka gabata, kuma wannan majalisa ba'a taɓa kamata da wani laifi ba a hukumance, majalisa ce wadda ta tara al'umma mabambanta kamar 'yan siyasa, jinin sarauta, dattijai, matasa, da sauran al'umma".

"saboda haka mun ka dawo wannan majalisar domin cika wannan alƙawari da muka dauka, kasancewar muna da damar yin haka.  saboda haka cike da fatan wannan Genaretor da muka damƙa maka, Allah ya sanya albarka da alheri a ciki, ya sa nan da shekara mai zuwa kaima ka baiwa wani".

A ƙarshe ya godewa wannan majalisar da kuma al'ummar da wannan majalisa ta tara, a bisa wannan gagarumar tarbo da aka samu daga wannan waje, tun daga karramawa da shayi na gaske, da kuma shimfiɗar fuska.

Haka a lokacin da aka bayar da turun magana ga shugaban majalisar ya nuna matuƙar farin cikinsa a bisa wannan namijin ƙoƙari, na bashi wannan abun neman abinci, sannan yayi kira ga sauran 'yan siyasa da masu hannu da shuni da suyi ko'i da halayyar Yazeed wajan taimakon al'umma gwargwadon hali. A ƙarshe yayi addu'ar Allah ya saka masa da mafificin alhari.

A lokacin bayar da wannan kyauta na lura sosai, da bayanai da wani jigo daga cikin dattawan majalisar yayi na cewa, basu  da abinda zasu iya cewa ga Yazeed sai dai fatan alheri, domin ya yi masu halacci da karamci a lokacin suka isa jihar Kaduna wajan gudanar da wasu ayyuka, Allah ya ƙaddara sun kayi kicibis da wajan saukar baƙi na (Alh Yazeed Shehu Ɗanfulani) a jihar  Kaduna, duk da kasancewar su basu san wannan waje na ɗan Zamfara ne ba, amma da Yazeed yaji ance 'yan Zamfara ne, nan take aka shigar da su wannan waje, kuma suka zauna a ciki, har tsawun lokaci da sun ka buƙaci komawa gida. Yace wani babban abun burgewa shine irin yadda wajan an rarraba shi ɓangare-ɓangare kuma an rubuta sunayen wasu daga cikin sunayen sassan jihar Zamfara.

Bayan kammala nashi jawabin wasu da dama sun gabatar da nasu jawaban, daga karshe sunyi addu'a da fatan alheri ga wannan tafiya mai cike da alheri.


Daga yanzu Kowane lokaci, al'ummar majalisar Himma Shayi  A Shirye Suke su bada tasu gudunmuwa, idan buƙatar hakan ta samu!

Daga Nura Mai Apple Media Reporter.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...