Skip to main content

WANE TSARI GWAMNATIN TARAYYA DA NA JIHOHI SUN KA YIWA MASU DAN KARAMIN KARFI, BAYAN SANYAWA KASA DA JIHOHI TA KUNKUMI, DON BAYAR DA KARIYA GA CUTAR KORONA?



Duk da kasancewar cutar Karona cuta ce mai matukar  hatsarin gaske, tun  daga saurin yaduwa kamar wutar daji, ga kuma saurin kisa, idan mu kayi tsinkaye ga dubban al'ummar da wannan cuta ta hallaka a yankuna daban-daban na duniya, wanda hakan ya sa hatta a kasashen duniya masu karfin fada aji, da kuma karfin tattalin arziki sun girgiza sosai a sanadiyar wannan cuta.

Iya binciken masani fannin lafiya da kuma bincike mai zurfi sun tabbatar da har kawowa wannan lokaci babu ainihin takamammen maganin wannan cuta mai toshe lunfashi. Wanda haka yasa kasashen duniya suke ci gaba da garkame kan iyakokinsu, domin takaita illar cutar.

Kasashe daban-daban na duniya suna fitar da wani tallafi na musamman domin bayarwa ga ilahirin al'ummarsu, wanda hakan zai rage masu radadin halin matsi da suke ciki, sakamakon killacesu da akayi a gida, har zuwa lokacin da gwamnatocin kasashen sun ka kaiyade fara zarga-zarga.

Tuni ita ma Najeriya na shiga cikin jerin gwanon gwamnatocin duniya wajen rufe kan iyakokinta, don kandagarkin cutar coronavirus mai saurin yaduwa. Hakan ya samo asali ne, saboda ganin irin yadda wannan kwayar cuta ke ci gaba da ruruwa a cikin kasar ta Najeriya.

Ko shakka babu mun yaba matuka ainun ga gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari hadi da ilahirin jerin gwanon gwamnoni baki daya akan irin matakan da sun ka dauka, na killace kasa, dama sassan kasar baki daya domin ta kaita wannan annoba.


Saura da mi, bayan cutar Korona, akwai wata cuta ta yunwa. Na tabbata kashi 80 cikin 100 na mutanen Najeriya Talakawa ne, wasu daga cikinsu suna cikin halin tsadar rayuwa, domin wasu sai sun fito sun nema sannan su koma su baiwa iyalansu.

Shin gwamnatin Najeriya wane tsari tayi ga irin wadannan bayin Allah? Kamar yadda mun ka sha gani a sauran wasu kasahe, inda ake bi ana tallafawa al'umma da kayan abinci. Yana da kyau gwamnatin tarayya ta fito da irin wannan tsarin domin rage radadin talaucin da yayi wa al'umma daurin gwarmai!

Haka jihohin da su kansu suka dauki matakin rufe iyakokin jihohinsu domin hanawa da yada cutar covid19, ko wane tsari sun ka yiwa al'ummarsu, wanda zai taimakawa jama'a kafin adadin tsawun makwannin da za a kwashe kafin bude kan iyakokin da zasu kasance a garkame?

Idan har an samar da wani tallafi ga bayin Allah marasa galihu, to lallai a tsaya ayi tsari mai kyau wanda tallafin zai kai ga wadanda aka bayar da tallafin dominsu, don kaucewa babba da jika!

Muna fatan Allah ya ta kaita wannan cuta, yayi mana maganinta. Wadanda sunka kamu Allah ya basu lafiya, wadanda basu kamu ba, Alah ya kare su da kamawa da wannan cuta mai tayar da hankali.

Daga Nura Mai Apple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020