Skip to main content

Zuwa ga mai girma Gwamnan Jihar Zamfara



Assalamu alaikum.

Bayan sallama irin ta addinin musulunci, cike da girmama a matsayina na talakanka, kuma wanda yake a karkashin jagorancinka a wannan jiha tamu mai albarka wanda bamu da wata jiha bayanta. Nake bayyana ra'ayi na, a bisa wannan nazari naka na ganin jihar Zamfara ta kece tsara a sauran jihohin da muke da su a cikin kasar nan na gina sabon gidan gwamnati la'akari da irin yadda aka barmu a baya ta gefen babban gida, mallakar gwamnati. Babu ko shakka wannan nazari ne mai kyau kuma abun so ne, kuma ci gaba ne mai alfanu, Allah ta'ala ya mana jagora, Amin!

Ba zan so na kaucewa daftarin tsarin dokar kasar nan ba, na damar da aka bawa 'yan kasa na fadin albarkacin baki, cikin sashe na 39 karamin sashe na kundin tsarin mulkin kasar nan. A kowane lokaci irinmu masu nazari da sharhi akan al'amurran yau da kullum ba'a rasa mu da tsegumi akan wasu abubuwa mabambanta akan abunda suka shafi kasar nan dama wasu jihohi wani lokacin ma har da wasu kasashen ketare.

Ranka ya Dade Sir! Hakika akwai wasu muhimman abubuwa da sun ka fi wannan aiki muhimmanci. Hakika aniyar Gwamnatinka na gina sabon katafaren gidan gwamnati wanda zai lakume zunzurutun kudi har Naira miliyan dubu bakwa 7 a wannan shekara ta 2020. Wani babban kuskure ne idan muka dubi irin yadda jihar bata gama tasowa ba daga cikin babban ƙalubalen da ta fuskanto cikin shekarun baya, tabbas waɗannan kuɗaɗe sunyi matukar yawa, kasancewer yanzu haka akwai wasu sassa a cikin jihar inda basu  da wadatattun ruwan sha, hadi wuraran shan magani, ballantana uwa uba wutar lantarki.


 A duk cikin kasar nan Zamfara ce kawai Jihar da bata da jami'a mallakar gwamnatin jiha. Mafi yawa daga cikin 'ya'yan talakawa basu iya karatu a jami'ar gwamnatin tarayya da muke da ita a cikin jihar nan. saboda rashin abin yi kuma ana bukatar karatun, zai kyautu matuka a fifita ta koma bayan wannan aiki, a nawa Nazarin!

Tun kafin aje ko ina a cikin babban birnin jihar wato Gusau har yanzu ba'a samu wadatattun ruwan sha ba, to ballantana ayi maganar wasu ƙananan hukumomi da sauran gundumomi zuwa ƙauyuka. Lallai ne mai girma gwamnan jihar Zamfara a sake dubawa haɗi da nazari akan wannan lamari, domin kana da matuƙar ƙima da kwarjini a idanun mutanan jihar Zamfara musamman talakawa.

Mun san cewa shi gyara abun so ne, to amma adadin kudin da wannan aiki zai ci zai bar wani wagegen giɓi a kasafin kuɗin wannan shekarar ta 2020, tattalin arziƙin jihar Zamfara baida ƙarfin da za'a iya fitar da waɗanannan ƙuɗaɗe ba tare da ya girgiza ba, idan mukayi  la'akari da jihar Zamfara bata da wasu manyan hanyoyin da kuɗaɗen shiga ke zuwa, kamar sauran wasu jihohi, irin Jihar Kano da Jihar legas, da wasu manyan jihohin ƙasar nan, muna roƙon mai girma gwamna a matsayinsa na mai kishin talaka yayi nazari mai zurfi a bisa wannan yunƙuri.


Wasu daga cikin ƙananan asibitocinmu suna matuƙar buƙatar muhimmiyar kulawa, musamman yadda za'a kawo marar lafiya, amma babu isassun jami'an kiyon lafiya. Sannan hanyoyin ƙarkara sunyi matuƙar lalacewa musamman idan yanayin damina ya zo. Wasu hanyoyi ba a iya biyarsu duk da tarin kasuwannin da ke cikinsu.

Haka fannin samar da ruwan sha wadatattu yankunan karkara suna da matuƙar buƙatar hakan suna buƙatar samar da fanfunan tuƙa-tuƙa ko manyan riyojin murtsatse, muna roƙo gareka mai girma gwamna! ya kamata hankalinka ya karkato a wannan fanni, domin ganin jihar ta samu ci gaba ta kowane fani hadi da mutanenta sun amfana da romon mulkin demokaradiyya. Allah ya baka ikon ganin wannan ra'ayi nawa, domin a dubi talaka da idon rahama. Fatan alheri ga reka, Allah ya ci gaba da yi maka jagora a cikin mulkinka.

 Nura Muhammad

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...