Skip to main content

RUGUNTSUMIN CHANZA SHEKA; hattara Zamfarawa da 'yan yaudara.

RUGUNTSUMIN CHANZA SHEKA; hattara Zamfarawa da 'yan yaudara.

Wani abu da ba kasafai ake yinsa ba kafatanin duniya kwata, inda banda Afrika musamman Najeriya, shine ribibin chanza sheka daga wannan jam'iyyar siyasa zuwa waccan, musamman idan aka samu chanjin gwamnati. Wasu suna daukar abun tamkar kasuwanci ko zuba jari a kasuwa, hakika wannan tunane, ko nace irin wannan safgar/ siga ta sha bam-ban da wasu kasashen duniya.

Idan muka yi nazari da kyau muka dubi kasar Amurka wadda ita ce Najeriya take kwaikwayo a falsafar tafiyar da al'amurran yau da kullum, musamman a fagen siyasa hadi da daftarin demokaradiyya, a kasar Amurka duk da yawan da take da shi da kuma fintikau da tayiwa wasu kasashen duniya, Amma jam'iyyun siyasar su biyu,  Publican da kuma Democratic, kuma sune suke ci gaba da mulkar kasar tun farkon samun 'yancin gashin kai har zuwa wannan lokaci da muke ciki.

Bari dai kar na wahalar da Mai karatu, kachokan bari naje wajen abinda nake son cewa domin Mai karatu ya fahimci inda na Mai da gaba.

Ina magana ne a kan jihar Zamfara, tun farkon samun assasa wannan jihar tana daya daga cikin Jihohin da suke fama da farfagandar siyasa, ko da yake wannan ne Karo na farko da aka samu juyin-juya-halin siyasa a jihar ta Zamfara. Inda jam'iyyar PDP ta samu damar karɓe ragamar jagorancin shugabancin jihar.


       Manyan jam'iyyun siyasar Najeriya


A gida irin na siyasa dole ne a samu mutane masu tsantseni domin hakan ne zai bada damar cimma dukkanin nasarar da ake buƙata, wajan fafutikar da ake don ganin a ciyar da jiha gaba.

To sai dai wani abin mamaki shine irin yadda wasu jiga-jigan waccan tsohuwar tafiyar suka fara juya akalarsu daga waccen tafiyar zuwa wannan. kuma sune suka san ciki da wajen waccan tsohowar gwamnatin, yanzu kuma sune suka fara juyowa suna dawowa cikin tafiyar wannan gwamnati, sannan ana karɓarsu ba tare da bin diddigin shin a lokacin da suna cikin waccen tafiyar ta tsohowar gwamnatin da ta shuɗe wace irin gudunmuwa suka baiwa al'umma, wadda kuma yanzu suke ganin suɓulewar damar ne ya sa su waiwaye domin su dawo cikin wannan tafiyar don ganin an ciyar da jiha a gaba.


Yana da kyau Gwamnatin jihar Zamfara da tayi dogon nazari akan masu ribibin sauya sheka daga wata jam'iyya zuwa wata musamman a jam'iyyar dake riƙe da madafun iko, don gudun yin kisto da kwarkwata, duk wani mai muradin kawo sauye-sauye a cikin al'umma zai iya bada kowace irin gudunmuwa ba kawai sai a jam'iyyar da ke mulki ba.

Tabbas daga cikin kowace al'umma akwai ɓata gari, musamman 'yan ɓata miya ba don asha ba.

Muna kira da babbar murya ga gwamnatin mai girma Gwamnan Jihar Zamfara (Rt Hon Bello Muhammad m.o.n Matawallen Maradun) da yayi taka tsantsan wajen shigar wasu cikin gwamnatinsa, saboda ganin irin yadda ya dauko tsare-tsare masu ma'ana, don ganin jihar nan ta samu cigaba ta kowane fanni.

A karshe ina addu'ar samun zaman lafiya mai dorewa a jihar Zamfara da Arewacin Najeriya da Najeriya da Duniya baki daya. Fatan alheri ga Gwamnatin Matawalle.


Comrd Nura Muhammad mai Apple Gusau 081333376020




Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

Ta kashe Mijin ta na aure

Ta kashe Mijin ta na aure Jami'an 'Yan Sanda sun damke wata mata mai shekara 42 ta kashe Mijin ta na aure a wata Unguwa a Garin Legas. Ana zargin Folashade Idoko da kashe Mijin ta a cikin gidan su. Jaridar Daily Post tace wannan mummunan abu ya faru ne a cikin Oto-Awori na Garin Legas. Marigayin dai Injiniya ne kuma tuni dai Jamia'an 'Yan Sanda su kayi ram da wannan mata. Mai gidan hayan da Iyalin su ke yace matar wanda malamar asibiti ce ta dade su na samun matsala da Mijin na ta amma yana hakuri. Kuma dai akwai kishin-kishin din cewa kishin jaraba ne ya sa ta kashe Mijin na ta. Matar dai tace tsautsayi aka samu wuka ta fadi a jikin sa ya mutu. Jami’an tsaro sun damke wani saurayi Ifeanyi Chukwu Maxwell Dike dauke da jikin wata yarinya da aka sace a makon jiya.