Skip to main content

Shirin tallafawa matasa na gwamnati Matawalle



Mai girma gwamnan jahar Zamfara, Hon (Dr.) Bello Mohammed Matawalle (Matawallen Maradun) ya kaddamar da shirin tallafawa matasa har su 229 marassa ayukkan yi har naira miliyan 81 a jahar Zamfara.

Bikin bude tallafin ya gudana ne a ofishin Fadama da ke Samuru Gusau.

Tallafin wanda aka baiwa matasa 229 a shirin  Fadama Wanda kacokan an bullo da shirin ne, Domin matasa Da mata da su ka Kammala karatu ba su da aikin yi Domin su dogara da kawunansu .

Mutun  229  da su ka amfana Da shirin sun fito daga kananan hukumomi 14 na jahar Zamfara. Wanda wasu za su mayar da hankali ga kiyon kaji,kiyon kifi da kuma noma.

Gwamnan ya bayyana cewa  Kudin tallafi ne ba bashi ba. An baiwa Matasan su ne, domin yin yakar zaman kashe wando ta hanyar yi kasuwanci ta yadda za su tallafi kansu har a samu cigaban tattalin arziki a jahar Zamfara.

Haka zalika gwamnan ya shawarci wadanda su ka samu wannan tallafi Da su yi amfani Da abunda su ka samu kamar yadda ya dace, domin cigaban kansu har su dauki wasu aiki.

Gwamna Matawalle ya kara Da cewa gwamnatinsa za ta cigaba Da aiki da masu son su tallafawa al'ummar jahar Zamfara ta fuskar noma da da sauran shiraruwa Da ake bullowa da su Domin taimakon Al'umma.

Yusuf Idris G
Babban Daraktan Watsa Labarai A Fadar Gwamnatin Jahar Zamfara.

Fassara: Abdulmalik Saidu Mai Biredi Tashar Bagu Gusau
02/07/2019

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.