Skip to main content

RASHIN SAMUN ALBASHI MA'AIKATA SUN KOKA




Rayuwar ma'aikacin gwamnati a Najeriya kamar rayuwar hannu baka hannu gwarya ce. mafi yawa daga cikin ma'aikatan gwamnati a wasu sassan Najeriya albashin nasu kawai sun ka dogara da shi, sannan ga tarin iyalai da 'yan uwa, ga sauran dawainiyar yau da kullum, sannan uwa uba ga yanayin kasar yadda take da tsadar rayuwa.

A jihar Zamfara mafi yawa daga cikin ma'aikatanta kachokan sun dogara ne da aikin gwamnati kawai, ga tarin iyalai da 'yan uwan ma'aikatan dakkanin dawainiyarsu sun jingina ta ga aikin na gwamnati.

Tun ana 20 wata ya kare ma'aikaci yake ta zumudin ganin karshen wata don ya anshi albashinsa, kasancewar duk lokacin da albashin zai zo 'yan kudaden albashin lassafaffi ne. 25 ga wata, ma'aikaci da zarar kararrawar wayarsa ta buga, yakan za bura ya duba domin ganin irin sakon da ya shigo a cikin wayar tasa.

Cikin ikon Allah yau 4 ga wata ma'aikacin gwamnati a jihar Zamfara bai amshi albashi ba. Ma'aikata da dama da na zanta dasu, sun bayyana min irin radadin da suke ji, sakamakon rashin shigowar albashin a hannu.

Wani bawan Allah da ya nemi na sakaya sunansa, ya bayyana min cewa iyalansa suna cikin halin ka-ka-ni-ka-yi sakamakon rashin albashin da yake saran zuwansa tun kafin karewar watan da ya gabata. Yace; ''wannan albashin shine kawai abinda na dogara da shi, banda wani abu ko wani kasuwanci da nake yi, bayan aikin gwamnati, na " basusuka da yawanl"l gaske, ina jiran albashin don na biya na kara karbar wasu, amma hakan ya citura''.

Duk da munsan gwamnati tana iya kokarinta wajen inganta walwala da jin dadin al'umma, to amma yana da kyau a dubi matsalar rashin biyan albashin ma'aikata da wuri don magance matsalar.

Muna fatan al'umma zasu samu ingantacciyar rayuwa a cikin wannan manufofi da gwamnatin PDP wadda ta kama aiki cikin watan jiya ke shirin ganin an samu.


Daga Nura Muhammad Mai Apple, Gusau.



Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020