Skip to main content

RASHIN SAMUN ALBASHI MA'AIKATA SUN KOKA




Rayuwar ma'aikacin gwamnati a Najeriya kamar rayuwar hannu baka hannu gwarya ce. mafi yawa daga cikin ma'aikatan gwamnati a wasu sassan Najeriya albashin nasu kawai sun ka dogara da shi, sannan ga tarin iyalai da 'yan uwa, ga sauran dawainiyar yau da kullum, sannan uwa uba ga yanayin kasar yadda take da tsadar rayuwa.

A jihar Zamfara mafi yawa daga cikin ma'aikatanta kachokan sun dogara ne da aikin gwamnati kawai, ga tarin iyalai da 'yan uwan ma'aikatan dakkanin dawainiyarsu sun jingina ta ga aikin na gwamnati.

Tun ana 20 wata ya kare ma'aikaci yake ta zumudin ganin karshen wata don ya anshi albashinsa, kasancewar duk lokacin da albashin zai zo 'yan kudaden albashin lassafaffi ne. 25 ga wata, ma'aikaci da zarar kararrawar wayarsa ta buga, yakan za bura ya duba domin ganin irin sakon da ya shigo a cikin wayar tasa.

Cikin ikon Allah yau 4 ga wata ma'aikacin gwamnati a jihar Zamfara bai amshi albashi ba. Ma'aikata da dama da na zanta dasu, sun bayyana min irin radadin da suke ji, sakamakon rashin shigowar albashin a hannu.

Wani bawan Allah da ya nemi na sakaya sunansa, ya bayyana min cewa iyalansa suna cikin halin ka-ka-ni-ka-yi sakamakon rashin albashin da yake saran zuwansa tun kafin karewar watan da ya gabata. Yace; ''wannan albashin shine kawai abinda na dogara da shi, banda wani abu ko wani kasuwanci da nake yi, bayan aikin gwamnati, na " basusuka da yawanl"l gaske, ina jiran albashin don na biya na kara karbar wasu, amma hakan ya citura''.

Duk da munsan gwamnati tana iya kokarinta wajen inganta walwala da jin dadin al'umma, to amma yana da kyau a dubi matsalar rashin biyan albashin ma'aikata da wuri don magance matsalar.

Muna fatan al'umma zasu samu ingantacciyar rayuwa a cikin wannan manufofi da gwamnatin PDP wadda ta kama aiki cikin watan jiya ke shirin ganin an samu.


Daga Nura Muhammad Mai Apple, Gusau.



Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.