Skip to main content

RASHIN SAMUN ALBASHI MA'AIKATA SUN KOKA




Rayuwar ma'aikacin gwamnati a Najeriya kamar rayuwar hannu baka hannu gwarya ce. mafi yawa daga cikin ma'aikatan gwamnati a wasu sassan Najeriya albashin nasu kawai sun ka dogara da shi, sannan ga tarin iyalai da 'yan uwa, ga sauran dawainiyar yau da kullum, sannan uwa uba ga yanayin kasar yadda take da tsadar rayuwa.

A jihar Zamfara mafi yawa daga cikin ma'aikatanta kachokan sun dogara ne da aikin gwamnati kawai, ga tarin iyalai da 'yan uwan ma'aikatan dakkanin dawainiyarsu sun jingina ta ga aikin na gwamnati.

Tun ana 20 wata ya kare ma'aikaci yake ta zumudin ganin karshen wata don ya anshi albashinsa, kasancewar duk lokacin da albashin zai zo 'yan kudaden albashin lassafaffi ne. 25 ga wata, ma'aikaci da zarar kararrawar wayarsa ta buga, yakan za bura ya duba domin ganin irin sakon da ya shigo a cikin wayar tasa.

Cikin ikon Allah yau 4 ga wata ma'aikacin gwamnati a jihar Zamfara bai amshi albashi ba. Ma'aikata da dama da na zanta dasu, sun bayyana min irin radadin da suke ji, sakamakon rashin shigowar albashin a hannu.

Wani bawan Allah da ya nemi na sakaya sunansa, ya bayyana min cewa iyalansa suna cikin halin ka-ka-ni-ka-yi sakamakon rashin albashin da yake saran zuwansa tun kafin karewar watan da ya gabata. Yace; ''wannan albashin shine kawai abinda na dogara da shi, banda wani abu ko wani kasuwanci da nake yi, bayan aikin gwamnati, na " basusuka da yawanl"l gaske, ina jiran albashin don na biya na kara karbar wasu, amma hakan ya citura''.

Duk da munsan gwamnati tana iya kokarinta wajen inganta walwala da jin dadin al'umma, to amma yana da kyau a dubi matsalar rashin biyan albashin ma'aikata da wuri don magance matsalar.

Muna fatan al'umma zasu samu ingantacciyar rayuwa a cikin wannan manufofi da gwamnatin PDP wadda ta kama aiki cikin watan jiya ke shirin ganin an samu.


Daga Nura Muhammad Mai Apple, Gusau.



Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...