Skip to main content

Makomar mabiya mazhabar shi'a a Najeriya



Babu shakka, kowa yasan Najeriya ya san Kasa ce mai yawan addinai daban-daban sannan kundin tsarin mulki na kasa a Najeriya yaba kowane addini damar yin addininsa ba tare da tsangwama, ko hantara ba, matukar ba yazo da wani abu wanda zai ci karo da saɓa Ƙa'ida ba, Najeriya ƙasar da ta baiwa dukkan 'yan ƙasar cikakkiyar damar ci gaba da rayuwa a cikin ƙasar ba tare da wani fargaba, ko shakku ba.
                   lokacin da suke zanga-zanga a Abuja


Tun lokacin da aka samu karon batta a tsakanin sojojin Najeriyar da 'ya'yan kungiyar 'yan uwa musulmi ta mabiya mazhabar shi'a a shekarar 2015 a birnin Zaria ta jihar Kaduna, ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula har zuwa wannan lokaci da muke ciki, rikicin wanda yayi sanadiyar ajalin gwamman rayuka haɗi da dukiyoyi, wani babban abun takaici ne da Allah waddai. Kuma yana daya daga cikin abinda ya mayar da hannun agogo baya, ta fuskar ƙoƙarin da ake wajen ganin ƙasar nan ta samu dauwamammen zaman lafiya haɗi da ci gaban Ƙasa.

To sai dai rikicin kwana-kwanan nan wanda ya gudana a babban birnin tarayya Abuja, shine mafi munin rikicin da munka gani, ta fuskar amfani da karfin da ya wuce ƙima na son shiga majalisar dattawan Kasar da karfin tuwo, wanda haka yayi sanadiyar mutuwar wani babban jami'in tsaro, haɗi da wani ɗan Jarida. A kan ƙoƙarin mabiya mazhabar shi'ar na son a saki jagoransu Sheikh Ibrahim Alzakkaky. Wanda ake cigaba da tsarewa akan wancen laifin da ake zarginsa da shi na sa magoya bayansa suyi fito-na-fito da hukuma.

            Lokacin da suke fito na fito da vyan sanda



Duk wanda yake a cikin kasar nan yasan cewa ɗaukar doka a hannu ba karamin kuskure ba ne, kuma taka doka ne daga cikin dokokin kasa, sanin ya kamata shine mutum ya yi amfani da abubuwa guda biyu, na farko shine; idan ya aikata abu, shin ba laifi bane a cikin addininsa? Na biyu shin abin nan da dan Adam zai aikata shin zaici karo da dokokin ƙasa, babu shakka duk mai amfani da irin waɗannan dabarun babu yadda za'ayi yayi abun tir da Allah waddai, har a ƙarshe ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakinin al'umma.

Kungiyar addini mai fafutikar watsa da'awa a cikin al'umma, basa faɗa ko tashin hankali da juna, duk mai ƙoƙarin ganin da'awarsa ta samu karɓuwa a cikin al'umma yana bi ne sannu a hanhali cikin lumana da kwanciyar hankali cikin tsanaki sannan a natse, domin mutane su gane hikimar da ke akwai a cikin addinin hakan zai kara ƙarfafa ma wasu mutane gwiwa suji suna sha'awar shiga, ba tare da kai ruwa rana ba.

Addinin musulunci bai barmu kara zube ba, ya koya mana yadda zamu yi mu'amala da al'umma daban-daban daga ciki har waɗanda ba addininmu guda da su ba, babu shakka addini musulunci baya ƙirƙirar tashin hankali, ko son rashin zaman lafiya a tsakanin al'umma maban-banta a duk inda mutum ya tsinci kansa.


Saka kungiyar a cikin jerin kungiyoyin 'yan ta'adda, yana da kyau mahukunta su tsaya suyi karatun ta natsu wajen amfani da dabaru da hikimomi, wajen nazarin hanyar da ya kamata abi, domin ganin yin haka ba zai kara ruruta wata wutar rikici ba, La'akari da yadda muke ganin abun zai shafi arewa ne, idan mukayi dubi mai kyau. Ga kungiyar masu tada ƙayar baya ta 'yan Boko Haram, haka ga ta masu satar shanu wadda ta juya zuwa ta masu garkuwa da mutane don karɓar kuɗin fansa, sannan yanzu ga rikicin kungiyar mabiya shi'a.


Yanzu lokaci ne da ya kamata a haɗu domin laluɓo hanyoyin samun zaman lafiya, kasancewar shine kashin bayan ci gaba kowace al'umma a duniya, saboda muna maraba da duk wata hanya da gwamnati take ganin ya dace abi domin samun zaman lafiya, muna kira da babbar murya ga 'ya'yan wannan kungiya da su san babu abinda yafi zama lafiya daɗi, sannan yana da kyau mu koyi yadda ake zama lafiya, don mu zauna lafiya har mu ciyar da ƙasar a gaba.

A ƙarshe muna addu'ar Allah ya tabbatar mana da abinda yafi zama alheri a cikin ƙasarmu Najeriya baki daya.

Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020