Skip to main content

FADAKARWA GA MATASANMU DA KE SHIRIN RUBUTA JARABAWAR JAMB 2020!



Muna amfani da damar Domin sanar da 'yan uwa matasa Da ke Da gudurin shiga jami'a. Kamar yadda mu ka sani dole ga Dan Najeriya ya yi Jarabawar share fagen shiga jam'iya wato Jamb Kafin ya samu gurbin karatu a jami'o'in kasarmu Najeriya.

Dan haka kenan Jarabawar na da matukar muhimmanci ko ma in ce dole ce. A shekarun Da su ka wuce, ba wasu dokoki da Kai'doji da su ka bullo Da su. Sai dai kullum Kara bullo da wasu ka'idoji su ke yi da zummar ko dai inganta Jarabawar ko ba ta tsaron kaucewa Sata ko fuskantar matsalolin da ke tusgowa.

Wanda a wannan shekarar Mai kamawa sun bullo da shirin yin amfani da lambobin katin shedar Dan kasa. Ma'ana ya zama wajibi ga duk Wanda zai rubuta jamb ya kasance ya mallaki katin shedar zama Dan kasa, Domin a cikin katin lambar ta ke. A Cewar hukumar hakan ya faru ne Dan kaucewa yin rigista fiye Da daya Da wasu ke yi.

Dan haka muna amfani da wannan damar mu sanar da 'yan uwa Da uwaye duk Wanda ya San wani NASA zai zana wannan Jarabawar ya hanzarta ziyartar ofishin yin katin shedar Dan kasa mafi kusa Da shi. Domin yin rigista.

Dan Allah mu yada wannan wannan sakon Dan amfanar 'yan uwanmu! Da ba su san da wannan sabon shirin ba.
Allah ya sa mu dace amin.


Daga Sufyanu Dan iya Gummi.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

KUNGIYAR MURYAR TALAKA TA BAYAR DA TALLAFIN KAYAN MAKARANTA, GA DALIBBAI DA KADDAMAR DA SHUWAGABANNINTA A KARAMAR HUKUMAR MARU!

A yau Talata 19-12-2017 kungiyar Muryar Talaka ta kasa Reshen Jahar Zamfara. Kai ziyara a Karamar hukumar Maru domin bayar da tallafin kayan karatu ga dalibbai a makarantun Gwamnati da ke wadannan karamar hukumar . A lokacin ziyarar wadda shugaban kungiyar na Jahar Zamfara, Comrade HAFIZU BALARABE GUSAU. ya jagoranta. Ya bayyana cewa, kungiyar Muryar Talaka ta bullo da wannan shirin ne, domin tallafawa, wajen cigaban bangaren ilimi a wannan jahar. Wanda hakan ne, ya sa kungiyar ta bullo da wannan shirin La'akkari da yadda wasu uwaye su ke da matukar rauni wajen daukar nauyin dawainiyar 'ya'yansu. Haka zalika hakan zai taimaka wajen habbaka sha'anin ILIMI a Jahar Zamfara. A lokacin da ya ke jawabi shugaban makarantar BANAGA SULE Primary school, Maru. Ya bayyana kungiyar muryar Talaka da cewa "Kungiya ce da ya kamata sauran kungiyoyi su yi koyi da ita. "Dan Haka ya kamata ku Kara jajircewa wajen aiki tukuru. Musamman ganin cewa kungiyar, ba kungiya ba ...