Skip to main content

FADAKARWA GA MATASANMU DA KE SHIRIN RUBUTA JARABAWAR JAMB 2020!



Muna amfani da damar Domin sanar da 'yan uwa matasa Da ke Da gudurin shiga jami'a. Kamar yadda mu ka sani dole ga Dan Najeriya ya yi Jarabawar share fagen shiga jam'iya wato Jamb Kafin ya samu gurbin karatu a jami'o'in kasarmu Najeriya.

Dan haka kenan Jarabawar na da matukar muhimmanci ko ma in ce dole ce. A shekarun Da su ka wuce, ba wasu dokoki da Kai'doji da su ka bullo Da su. Sai dai kullum Kara bullo da wasu ka'idoji su ke yi da zummar ko dai inganta Jarabawar ko ba ta tsaron kaucewa Sata ko fuskantar matsalolin da ke tusgowa.

Wanda a wannan shekarar Mai kamawa sun bullo da shirin yin amfani da lambobin katin shedar Dan kasa. Ma'ana ya zama wajibi ga duk Wanda zai rubuta jamb ya kasance ya mallaki katin shedar zama Dan kasa, Domin a cikin katin lambar ta ke. A Cewar hukumar hakan ya faru ne Dan kaucewa yin rigista fiye Da daya Da wasu ke yi.

Dan haka muna amfani da wannan damar mu sanar da 'yan uwa Da uwaye duk Wanda ya San wani NASA zai zana wannan Jarabawar ya hanzarta ziyartar ofishin yin katin shedar Dan kasa mafi kusa Da shi. Domin yin rigista.

Dan Allah mu yada wannan wannan sakon Dan amfanar 'yan uwanmu! Da ba su san da wannan sabon shirin ba.
Allah ya sa mu dace amin.


Daga Sufyanu Dan iya Gummi.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020