Skip to main content

A dakatar ko a tsaftacce sana'ar fina-finan hausa




Yana da kyau gwamnatin Najeriya ta dubi yiyuwar dakatar da sana'ar fina-finan hausa la'akari da yadda take taka rawa wajen gurɓacewar tarbiyyar malam Bahaushe. Ko a dauki matakai na musamman da suka kamata wajen tsaftacceta. mafi yawa daga cikin abubuwan al'ajabi da suke wakana a daidai wannan lokaci, ana kwaikwayon kaso mai tsoka daga cikin fina-finan da ake kallo.


Babbar barazanar da hakan ke haifarwa akwai ƙoƙarin jinginar da al'adar hausawa, haɗi da shi go da wasu baƙin al'adu da suka ci karo da addinin Musulunci ta sigogi mabanbanta.

Irin yadda aka san malam bahaushe da kunya da kamun kai da nuna halin dattako da ɗa'a ga har waɗanda ba kabilarsa ba, amma hakan yana shirin ɓacewa ɓat ! Saboda shigowar wasu baƙin al'adu da muke kalla a cikin fina-finai, yana da matuƙar alfanu a dubi wannan gagarumar matsala.


Mafi yawa daga cikin kaso mai tsoka na fina-finan hausa basu koyama al'umma yadda ake tarbiyya, sai dai nuna yadda ake lalata ta.


Babban abun taikaici ne ace mace bahaushiyya tana iya daukar makami da niyar hallaka abokin zamanta, ma'ana mijinta ko abokiyar zamanta, ba ta tunanin makomarta a matsayinta na musulma, kuma mace wadda ake tunanen samun tarbiyya daga wajenta.

A nan ina magana ne ga fina-finai na hausa kawai, saboda sune namu, kuma ake sarrafawa a cikin mu, kuma kamar yadda suke faɗa suna yi ne, domin inkiya, ko hannunka mai sanda, ko nuni, ko izina a kan faruwar wani abu. Muyi nazari akan illar ba wai abinda ake samu cikinta ba.


Muna kira da babbar murya ga maga'isa da su dubi wannan lamari, kuma suyi nazari a kai domin samun mafita, idan har hana hakan ba zai samu ba, lallai ya kamata a tsaftacceta, domin samun gyaruwar al'umma.

 Nura Mai Apple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020