Skip to main content

YA KAMATA A KOMA A HUTA ZAIFI DOMIN BAIWA WASU DAMAR MAYE GURBINKA!



Tun 1999 ake damawa da Kai a siyasar jihar nan, tun kafin zamanka a kujerar gwamna har ya kasance ka zama gwamna Mai cikakken iko a duk fadin jihar ta Zamfara, bayan kwashe shekaru Hudu kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar nan ya tanada, kuma ka nuna bukatar sake komawa kujerar jagorancin jihar a 2003 kuma ka samu damar zama gwamna a wa'adi na biyu ka ci gaba da jan ragamar jagorancin jihar har zuwa karshen zangon da aka tanadarwa kujerar gwamna a Najeriya.



Bayan nan ka tsinduma cikin neman kujerar Sanata a yankinka da ke Zamfara ta yamma a shekara ta 2007, bayan saukarka a kujerar gwamna a wancen lokacin, kuma Allah cikin ikonSa ka samu damar zuwa majalisar dattawa a shekara 2007 din, ka share shekaru Hudu cur !  mu dai babu wani abun kirki da mukaji ko muka gani kayiwa yankin naka, domin jindadi hadi da walwalar Al'ummarka.


Bayan nan ka dawo neman mukamin  zama Sanata a wa'adi na biyu, kuma ka samu nasarar komawa a zauran majalisar dattawan a shekara 2011 a haka ka share shekaru Hudu babu komai wanda Al'ummar da Kake wakilta zasu bugi girjin cewa sun samu daga wajenka, kasancewar ka samu dukkanin goyon baya daga talakawan jihar baki daya Wanda kuma hakan ya samo asali ne tun lokacin da kana gwamnan jihar ta Zamfara, saboda yunkurinka wajen dabbak'a Shari'ar musulunci, Wanda Ta sanadiyar haka Zamfarar ta zama abun duba da  k'ima a cikin jihojin Najeriya hadi da wasu kasashe masu sha'awar addinin musulunci.



Sannan bayan kaiwa karshen wa'adinka na 2015 ka Kara neman komawa kujerar jagorancin yankinka daga 2015 zuwa 2019 kuma ka samu cikakkiyar nasarar hakan, sanin kowane dan jihar Zamfara ne a matsayinka na shugaban limamin chanji a jihar Zamfara, kana da kowace irin dama wadda zaka iya amfani da ita domin gabatar da Kira "Motion" a Majalisa domin sanin halin da yankinka yake ciki na rashin tsaro domin samun dauki da agajin gaggawa, Amma kayi biris! Ka Kasa cewa uffan! a kan irin abinda yake faruwa a yankin naka Wanda kuma ya sabawa abinda aka tura ka dominsa.


Duk da haka a cikin wannan zango na 2019 kayi iya kokarinka domin ganin ka marawa Wanda talakawan jihar  basu so baya, Amma cikin iyawar Allah hakan bai samu ba, yanzu kuma gashi kwatsam sai muka ganka a cikin gidan gwamnati, ko shakka babu kanmu ya dauran matuka inda muka cigaba da dasa ayar tambaya wa junanmu kasancewar ba mu san takamammen abinda ya Kai ka ba.

 Idon kana son cigaban jihar nan ya zama wajibi ka koma gyefe kabar wannan sabuwar gwamnati ta yi shirinta Wanda take ganin ya kamata domin kai wannan jihar ga tudunbun tsira.


Nagode


Daga Nura Mai Apple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

Ta kashe Mijin ta na aure

Ta kashe Mijin ta na aure Jami'an 'Yan Sanda sun damke wata mata mai shekara 42 ta kashe Mijin ta na aure a wata Unguwa a Garin Legas. Ana zargin Folashade Idoko da kashe Mijin ta a cikin gidan su. Jaridar Daily Post tace wannan mummunan abu ya faru ne a cikin Oto-Awori na Garin Legas. Marigayin dai Injiniya ne kuma tuni dai Jamia'an 'Yan Sanda su kayi ram da wannan mata. Mai gidan hayan da Iyalin su ke yace matar wanda malamar asibiti ce ta dade su na samun matsala da Mijin na ta amma yana hakuri. Kuma dai akwai kishin-kishin din cewa kishin jaraba ne ya sa ta kashe Mijin na ta. Matar dai tace tsautsayi aka samu wuka ta fadi a jikin sa ya mutu. Jami’an tsaro sun damke wani saurayi Ifeanyi Chukwu Maxwell Dike dauke da jikin wata yarinya da aka sace a makon jiya.