Skip to main content

YA KAMATA A KOMA A HUTA ZAIFI DOMIN BAIWA WASU DAMAR MAYE GURBINKA!



Tun 1999 ake damawa da Kai a siyasar jihar nan, tun kafin zamanka a kujerar gwamna har ya kasance ka zama gwamna Mai cikakken iko a duk fadin jihar ta Zamfara, bayan kwashe shekaru Hudu kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar nan ya tanada, kuma ka nuna bukatar sake komawa kujerar jagorancin jihar a 2003 kuma ka samu damar zama gwamna a wa'adi na biyu ka ci gaba da jan ragamar jagorancin jihar har zuwa karshen zangon da aka tanadarwa kujerar gwamna a Najeriya.



Bayan nan ka tsinduma cikin neman kujerar Sanata a yankinka da ke Zamfara ta yamma a shekara ta 2007, bayan saukarka a kujerar gwamna a wancen lokacin, kuma Allah cikin ikonSa ka samu damar zuwa majalisar dattawa a shekara 2007 din, ka share shekaru Hudu cur !  mu dai babu wani abun kirki da mukaji ko muka gani kayiwa yankin naka, domin jindadi hadi da walwalar Al'ummarka.


Bayan nan ka dawo neman mukamin  zama Sanata a wa'adi na biyu, kuma ka samu nasarar komawa a zauran majalisar dattawan a shekara 2011 a haka ka share shekaru Hudu babu komai wanda Al'ummar da Kake wakilta zasu bugi girjin cewa sun samu daga wajenka, kasancewar ka samu dukkanin goyon baya daga talakawan jihar baki daya Wanda kuma hakan ya samo asali ne tun lokacin da kana gwamnan jihar ta Zamfara, saboda yunkurinka wajen dabbak'a Shari'ar musulunci, Wanda Ta sanadiyar haka Zamfarar ta zama abun duba da  k'ima a cikin jihojin Najeriya hadi da wasu kasashe masu sha'awar addinin musulunci.



Sannan bayan kaiwa karshen wa'adinka na 2015 ka Kara neman komawa kujerar jagorancin yankinka daga 2015 zuwa 2019 kuma ka samu cikakkiyar nasarar hakan, sanin kowane dan jihar Zamfara ne a matsayinka na shugaban limamin chanji a jihar Zamfara, kana da kowace irin dama wadda zaka iya amfani da ita domin gabatar da Kira "Motion" a Majalisa domin sanin halin da yankinka yake ciki na rashin tsaro domin samun dauki da agajin gaggawa, Amma kayi biris! Ka Kasa cewa uffan! a kan irin abinda yake faruwa a yankin naka Wanda kuma ya sabawa abinda aka tura ka dominsa.


Duk da haka a cikin wannan zango na 2019 kayi iya kokarinka domin ganin ka marawa Wanda talakawan jihar  basu so baya, Amma cikin iyawar Allah hakan bai samu ba, yanzu kuma gashi kwatsam sai muka ganka a cikin gidan gwamnati, ko shakka babu kanmu ya dauran matuka inda muka cigaba da dasa ayar tambaya wa junanmu kasancewar ba mu san takamammen abinda ya Kai ka ba.

 Idon kana son cigaban jihar nan ya zama wajibi ka koma gyefe kabar wannan sabuwar gwamnati ta yi shirinta Wanda take ganin ya kamata domin kai wannan jihar ga tudunbun tsira.


Nagode


Daga Nura Mai Apple

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...